< Ayuba 24 >

1 “Domin me Maɗaukaki ba zai sa ranar shari’a ba? Don me waɗanda suka san shi suke faman samun irin ranakun nan?
מדוע משדי לא נצפנו עתים וידעו לא חזו ימיו׃
2 Mugaye suna satar fili ta wurin matsar da duwatsun da aka yi iyaka da su; suna satar dabbobi su kuma yi kiwon su.
גבלות ישיגו עדר גזלו וירעו׃
3 Suna ƙwace wa marayu jakunansu suna kuma ƙwace wa gwauruwa sa don suna binta bashi.
חמור יתומים ינהגו יחבלו שור אלמנה׃
4 Suna ture matalauta daga hanya suna kuma sa dole matalautan ƙasar su ɓoye.
יטו אביונים מדרך יחד חבאו עניי ארץ׃
5 Kamar jakunan jeji a hamada, matalauta suna aikin neman abinci gonaki marasa amfani suna tanada abinci wa’ya’yansu.
הן פראים במדבר יצאו בפעלם משחרי לטרף ערבה לו לחם לנערים׃
6 Suna girbi a gonakin da ba nasu ba, suna yin kala a gonar inabi ta mugaye.
בשדה בלילו יקצירו וכרם רשע ילקשו׃
7 Don ba su da tufafi, sukan kwana tsirara; ba su da wani abin da zai rufe su cikin sanyi.
ערום ילינו מבלי לבוש ואין כסות בקרה׃
8 Sun jiƙe sharkaf da ruwan da yake kwararowa daga duwatsu, sun rungume duwatsu don rashin wurin fakewa.
מזרם הרים ירטבו ומבלי מחסה חבקו צור׃
9 Ana ƙwace jinjiri mai shan mama; ana ƙwace ɗan yaron matalauci don biyan bashi.
יגזלו משד יתום ועל עני יחבלו׃
10 Don ba su da tufafi suna yawo tsirara; suna dakon dammunan hatsi amma duk da haka suna cikin shan yunwa.
ערום הלכו בלי לבוש ורעבים נשאו עמר׃
11 Suna matse zaitun a cikin kunyoyi suna kuma matse ruwan inabi daga’ya’yan inabi, duk da haka suna fama da ƙishi.
בין שורתם יצהירו יקבים דרכו ויצמאו׃
12 Ana jin nishin masu mutuwa daga birni, kuma rayukan waɗanda aka ji musu rauni suna kuka suna kira don taimako. Amma bai ba wani laifi ba.
מעיר מתים ינאקו ונפש חללים תשוע ואלוה לא ישים תפלה׃
13 “Akwai waɗanda suke yi wa haske tawaye, waɗanda ba su san hanyoyinsa ba ko kuma ba su taɓa bin hanyoyinsa ba.
המה היו במרדי אור לא הכירו דרכיו ולא ישבו בנתיבתיו׃
14 Sa’ad da hasken yini ya tafi, mai kisankai yakan tashi; yă je yă kashe matalauta da masu bukata; a cikin dare yake shigowa kamar ɓarawo.
לאור יקום רוצח יקטל עני ואביון ובלילה יהי כגנב׃
15 Idanun mazinaci suna jiran yamma ta yi sosai; yana tunani cewa, ‘Ba wanda zai gan ni,’ sai kuma yă ɓoye fuskarsa.
ועין נאף שמרה נשף לאמר לא תשורני עין וסתר פנים ישים׃
16 Cikin duhu mutane suna fasa gidaje, amma da rana sukan kulle kansu; ba sa so wani abu yă haɗa su da haske.
חתר בחשך בתים יומם חתמו למו לא ידעו אור׃
17 Gama dukansu, duhu mai yawa shi ne safiyarsu; suna abokantaka da razanar duhu.
כי יחדו בקר למו צלמות כי יכיר בלהות צלמות׃
18 “Duk da haka kamar abu marar nauyi suke a kan ruwa; gefen ƙasar da suke, an la’anta ta, yadda ba wanda yake zuwa gonar inabinsu.
קל הוא על פני מים תקלל חלקתם בארץ לא יפנה דרך כרמים׃
19 Kamar yadda zafi da fări suke shanye ƙanƙarar da ta narke, haka kabari zai ƙwace waɗanda suka yi zunubi. (Sheol h7585)
ציה גם חם יגזלו מימי שלג שאול חטאו׃ (Sheol h7585)
20 Waɗanda suka haife su za su manta da su, tsutsotsi za su cinye su; ba za a sāke tunawa da mugaye ba amma an sare su kamar itace.
ישכחהו רחם מתקו רמה עוד לא יזכר ותשבר כעץ עולה׃
21 Suna cutar macen da ba ta da ɗa, suna nuna wa gwauruwa rashin alheri.
רעה עקרה לא תלד ואלמנה לא ייטיב׃
22 Amma Allah cikin ikonsa yakan kawar da masu ƙarfi, ko da yake sun yi ƙarfi, ba su da tabbacin rayuwa.
ומשך אבירים בכחו יקום ולא יאמין בחיין׃
23 Mai yiwuwa zai bar su su zauna cikin kwanciyar hankali, amma idanunsa suna kansu.
יתן לו לבטח וישען ועיניהו על דרכיהם׃
24 Sukan samu cin nasara na ɗan lokaci, amma kuma za su ɓace; za su fāɗi a tattara su kamar sauran; za a datse su kamar kan hatsi.
רומו מעט ואיננו והמכו ככל יקפצון וכראש שבלת ימלו׃
25 “In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”
ואם לא אפו מי יכזיבני וישם לאל מלתי׃

< Ayuba 24 >