< Ayuba 22 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Y respondió Elifaz Temanita, y dijo:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
¿Traerá el hombre provecho a Dios? porque el sabio a sí mismo aprovecha.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
¿Tiene su contentamiento el Omnipotente en que tú seas justificado? ¿o le viene algún provecho de que tú hagas perfectos tus caminos?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
¿Si porque te teme, te castigará, y vendrá contigo a juicio?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Por cierto tu malicia es grande: y tus maldades no tienen fin.
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Porque prendaste a tus hermanos sin causa, e hiciste desnudar las ropas de los desnudos.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
No diste de beber agua al cansado, y al hambriento detuviste el pan.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Empero el violento tuvo la tierra, y el honrado habitó en ella.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Las viudas enviaste vacías, y los brazos de los huérfanos fueron quebrados,
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Por tanto hay lazos al derredor de ti, y te turba espanto repentino:
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
O tinieblas, porque no veas; y abundancia de agua te cubre.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
¿No está Dios en la altura de los cielos? Mira la altura de las estrellas como son altas.
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
¿Dirás pues: Qué sabe Dios? ¿cómo juzgará por medio de la oscuridad?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Las nubes son su escondedero, y no ve: y por el cerco del cielo se pasea.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
¿Quieres tú guardar la senda antigua, que pisaron los varones perversos?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Los cuales fueron cortados antes de tiempo: cuyo fundamento fue como un río derramado:
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Que decían a Dios: Apártate de nosotros: ¿y qué nos ha de hacer el Omnipotente?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Habiendo él henchido sus casas de bienes. Por tanto el consejo de ellos lejos sea de mí.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Verán los justos, y gozarse han, y el inocente los escarnecerá.
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
¿Fue cortada nuestra substancia, habiendo consumido el fuego el resto de ellos?
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Ahora pues conciértate con él, y tendrás paz, y por ello te vendrá bien.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Toma ahora la ley de su boca, y pon sus palabras en tu corazón.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Si te tornares hasta el Omnipotente, serás edificado: alejarás de tu tienda la iniquidad.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
Y tendrás más oro que tierra, y como piedras de arroyos, oro de Ofir.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Y tu oro será el Todopoderoso; y tendrás plata a montones.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Porque entonces te deleitarás en el Omnipotente, y alzarás a Dios tu rostro.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Orarás a él, y él te oirá, y pagarás tus votos.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Y determinarás la cosa, y serte ha firme, y sobre tus caminos resplandecerá luz.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Cuando los otros fueren abatidos, dirás tú: Ensalzamiento: y al humilde de ojos salvará.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Un inocente escapará una isla: y en la limpieza de tus manos será guardada.