< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Entonces Elifaz el temanita respondió y dijo:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
“¿Cómo puede alguien ser de ayuda a Dios? Incluso los sabios sólo se ayudan a sí mismos.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
¿Acaso le sirve de algo al Todopoderoso que seas una buena persona? ¿Qué gana él si haces lo correcto?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
¿Acaso te corrige y te acusa por tu reverencia?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
No ¡Es porque eres muy malvado! ¡Tus pecados son interminables!
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Sin motivo alguno tomaste la ropa de tu hermano como garantía de una deuda y lo dejaste desnudo.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Le negaste el agua al sediento y alimento al hambriento.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
¿Es que acaso la tierra le pertenece a los poderosos, y sólo los privilegiados tienen derecho a vivir en ella?
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Has despedido a las viudas con las manos vacías; has aplastado los brazos extendidos de los huérfanos, que pedían ayuda.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Por eso estás rodeado de trampas para atraparte, y por eso de repente te asusta el terror.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Por eso está tan oscuro que no puedes ver, y por eso sientes que te ahogas.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
“¿Acaso Dios no vive en el cielo más alto y mira hasta las estrellas más altas?
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Pero tú preguntas: ‘¿Qué sabe Dios? ¿Cómo puede ver y juzgar lo que ocurre aquí abajo, en la oscuridad?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Unas densas nubes lo cubren para que no pueda ver nada mientras camina por el cielo’.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
“¿Por qué insistes en seguir el pensamiento tradicional de los malvados?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Fueron llevados antes de tiempo; todo lo que habían construido fue arrasado.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Habían dicho a Dios: ‘¡Vete lejos! ¿Qué puede hacernos el Todopoderoso?’
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Y, sin embargo, era él quien había llenado sus casas de bienes; pero no aceptaba su manera de pensar”.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
“Los que hacen el bien se alegran cuando ven la destrucción de los malvados, y los inocentes se burlan de ellos,
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
diciendo: ‘Nuestros enemigos han sido destruidos, y el fuego ha quemado todo lo que queda de ellos’.
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
“Vuelve a Dios y reconcíliate con él, y volverás a ser próspero.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Escucha lo que te dice y no olvides sus palabras.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Si te vuelves a Dios serás restaurado. Si renuncias a tu vida pecaminosa
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
y dejas tu amor por el dinero y el deseo de posesiones,
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
entonces el Todopoderoso será tu oro y tu plata preciosa.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
“Entonces te deleitarás en el Todopoderoso y podrás darle la cara sin sentirte avergonzado.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Orarás a él, y él te escuchará, y cumplirás tus promesas a él.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Todo lo que decidas hacer tendrá éxito, y dondequiera que vayas, la luz brillará sobre ti.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Cuando otros se humillen y digas: ‘Por favor, ayúdales’, Dios los salvará.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Dios salva a los inocentes, y tú te salvarás si haces lo que es justo”.

< Ayuba 22 >