< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Отвещав же Елифаз Феманитин, рече:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
не Господь ли есть научаяй разуму и хитрости?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Ибо кое попечение Господу, аще ты был еси делы непорочен? Или (кая) польза, яко прост творити будеши путь твой?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Или опасение имея от тебе обличит тя и внидет с тобою в суд?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Еда злоба твоя есть не многа? Безчисленнии же твои суть греси?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
В залог бо имал еси от братии твоея вотще, одежду же нагих отнимал еси,
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
ниже водою жаждущих напоил еси, но алчущих лишил еси хлеба:
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
удивлялся же еси неких лицу и повергал еси убогих на земли:
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
вдовицы же отпустил еси тщы и сироты озлобил еси.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Сего ради обыдоша тя сети, и поспеши на тя рать велика:
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
свет тебе тма бысть, уснувшаго же вода тя покры.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Еда на высоких живый не призирает? Укоризною же возносящихся смири.
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
И рекл еси: что разуме Крепкий? Или во мраце разсудит?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Облак покров Его, и неувидимь будет, и круг небесе обходит.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Еда стезю древнюю сохраниши, в нюже ходиша мужие неправедни,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
иже яти быша прежде времене? Река текущая основания их,
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
глаголющии: что сотворит нам Господь? Или что нанесет на ны Вседержитель?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Иже исполнил есть домы их благими: совет же нечестивых далече от Него.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Видевше праведницы возсмеяшася, непорочен же глумляшеся им:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
не погибе ли имение их, и останки их пояст огнь?
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Буди убо тверд, аще претерпиши, потом плод твой будет во благих.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Приими же из уст Его изречение и восприими словеса Его в сердце твое.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Аще же обратишися и смириши себе пред Господем, и далече сотвориши от жилища твоего неправду,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
и положен будеши на персти в камени, и якоже камень потока Офирска.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Будет убо тебе Вседержитель помощник от враг, чиста же сотворит тя якоже сребро разжжено,
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
потом дерзновение возимееши пред Богом, воззрев весело на небо.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Помольшуся же тебе к Нему, услышит тя, даст же ти обеты твоя воздати,
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
устроит же ти жилище правды, на путех же твоих будет свет:
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
яко смирил еси себе, тогда речеши: вознесеся, и поникша очима спасет,
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
избавит неповиннаго, и спасешися чистыма рукама твоима.

< Ayuba 22 >