< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Da tok Elifas fra Teman til orde og sa:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Kan vel en mann være til gagn for Gud? Nei, bare sig selv gagner den forstandige.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Er det til nogen nytte for den Allmektige at du er rettferdig, eller til nogen vinning at du vandrer ulastelig?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Er det for din gudsfrykts skyld han refser dig eller går i rette med dig?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Er ikke din ondskap stor og dine misgjerninger uten ende?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Du tok jo pant av dine brødre uten grunn og drog klærne av de nakne.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Du gav ikke den trette vann å drikke, og den sultne nektet du brød.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Men den som gikk frem med vold, han fikk landet i eie, og den som var høit aktet, bodde i det.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Enker har du latt fare tomhendt, og farløses armer blev knust.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Derfor er det snarer rundt omkring dig, og en hastig redsel forferder dig.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Eller ser du ikke mørket og den vannflom som dekker dig?
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Er ikke Gud høi som himmelen? Og se de øverste stjerner, hvor høit de står!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Og du sier: Hvad vet Gud? Kan han vel dømme gjennem mørket?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Skyene er et dekke for ham, så han ikke ser noget, og på himmelens hvelving vandrer han.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Vil du følge den sti som syndens menn vandret på i de gamle dager,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
de som blev bortrykket før tiden, og under hvis føtter grunnen fløt bort som en strøm,
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
de menn som sa til Gud: Vik fra oss, og som spurte hvad den Allmektige vel skulde kunne gjøre for dem,
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
enda han hadde fylt deres hus med det som var godt? - Men de ugudeliges tanker er lang fra mine tanker. -
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
De rettferdige så det og gledet sig, og de uskyldige spottet dem:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
Sannelig, våre fiender er tilintetgjort, og ild har fortært deres overflod.
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Forlik dig nu med ham, så vil du få fred! Og så skal lykke times dig.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Ta imot lærdom av hans munn og legg dig hans ord på hjerte!
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Vender du om til den Allmektige, da skal din lykke bli bygget op igjen; men du må få urett bort fra dine telt.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
Kast ditt gull i støvet og ditt Ofir-gull blandt bekkenes stener!
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Så skal den Allmektige være ditt gull, være som dynger av sølv for dig,
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
for da skal du glede dig i den Allmektige og løfte ditt åsyn til Gud.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Du skal bede til ham, og han skal høre dig, og du skal opfylle dine løfter,
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
og setter du dig noget fore, da skal det lykkes for dig, og over dine veier skal det skinne lys;
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
når de fører nedover, skal du si: Opover! Han skal frelse den som slår sitt øie ned;
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
han skal redde endog den som ikke er uskyldig; ved dine henders renhet skal han bli reddet.

< Ayuba 22 >