< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
U-Elifazi umThemani wasephendula wathi:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
“Umuntu angasiza uNkulunkulu na? Lesihlakaniphi uqobo kambe singamsiza na?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Bekungamupha ntokozo bani uSomandla ukulunga kwakho na? Ubengazuzani ngabe kuthiwa kawulasici na?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Yikumesaba kwakho yini akukhuzela khona lakwethesela khona amacala na?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Kabubukhulu ububi bakho na? Lezono zakho angithi kazipheli na?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Wawubiza isibambiso kubafowenu kungelasizatho; uhlubula abantu izigqoko zabo basale beze.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Abakhatheleyo wawubancitsha amanzi, abalambileyo ungabaphi ukudla,
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
lanxa wena wawuyindoda elamandla, ulepulazi, indoda ehlonitshwayo, uphila kulo.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Abafelokazi wabaxotsha ungabaphanga lutho izintandane waziqeda amandla.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Kungenxa yalokho usuhanqwe yimijibila, usuhlukuluzwa luhlupho masinyane,
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
yikho kumnyama kangaka ungasaboni, njalo yikho ususibekelwa zimpophoma zamanzi.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
UNkulunkulu kakho esiqongweni samazulu na? Ake ubone phela ukuthi ziphakeme njani izinkanyezi ezisesiqongweni!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Kodwa wena uthi, ‘UNkulunkulu wazini? Angahlulela phakathi komnyama onje?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Usithwe ngamayezi amakhulu, ngakho kasiboni nxa ehambahamba ezulwini eliphezulu.’
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Wena-ke uzakwalela endleleni endala na eseyahanjwa ngababi?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Bedluliswa singakafiki isikhathi sabo, izisekelo zabo zakhukhulwa nguzamcolo.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Bathi kuNkulunkulu, ‘Tshiyana lathi! USomandla angasenzani na?’
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Ikanti kunguye owagcwalisa izindlu zabo ngezinto ezinhle, ngakho kangingeni ezelulekweni zababi.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Abalungileyo bayakubona lokho bathokoze; abangelacala bayabahleka bathi,
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
‘Ngempela izitha zethu zichithiwe, lokuseleyo kwenotho yazo sekubhuqwe ngumlilo.’
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Zehlise kuNkulunkulu ukuze uwelelane laye; ngaleyondlela ukuphumelela kuzakuza kuwe.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Yamukela iziqondiso eziphuma emlonyeni wakhe, amazwi akhe uwabeke enhliziyweni yakho.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Nxa ubuyela kuSomandla, uzavuselelwa; nxa ususa ububi bube kude lethente lakho
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
lomthuso wakho uwulahlele othulini, igolide lakho lase-Ofiri ulilahlele emadwaleni ezifuleni,
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
lapho-ke uSomandla uzakuba ligolide lakho, lesiliva esikhethekileyo kuwe.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Ngempela uzazuza ukuthokoza kuSomandla uphakamisele ubuso bakho kuNkulunkulu.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Uzakhuleka kuye, yena akuzwe, njalo uzagcwalisa izifungo zakho.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Lokho okumisileyo kuzakwenziwa, lokukhanya kuzazikhanyisa izindlela zakho.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Nxa abantu besehliswa ubususithi, ‘Baphakamiseni!’ lapho-ke uzabasiza abahlulukelweyo.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Uzabasiza lalabo abonayo, abazakhululwa ngenxa yokubamsulwa kwakho.”

< Ayuba 22 >