< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Respondens autem Eliphaz Themanites, dixit:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
[Numquid Deo potest comparari homo, etiam cum perfectæ fuerit scientiæ?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Quid prodest Deo, si justus fueris? aut quid ei confers, si immaculata fuerit via tua?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Numquid timens arguet te, et veniet tecum in judicium,
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
et non propter malitiam tuam plurimam, et infinitas iniquitates tuas?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Abstulisti enim pignus fratrum tuorum sine causa, et nudos spoliasti vestibus.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Aquam lasso non dedisti, et esurienti subtraxisti panem.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
In fortitudine brachii tui possidebas terram, et potentissimus obtinebas eam.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Viduas dimisisti vacuas, et lacertos pupillorum comminuisti.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Propterea circumdatus es laqueis, et conturbat te formido subita.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Et putabas te tenebras non visurum, et impetu aquarum inundantium non oppressum iri?
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
an non cogitas quod Deus excelsior cælo sit, et super stellarum verticem sublimetur?
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Et dicis: Quid enim novit Deus? et quasi per caliginem judicat.
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Nubes latibulum ejus, nec nostra considerat, et circa cardines cæli perambulat.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Numquid semitam sæculorum custodire cupis, quam calcaverunt viri iniqui,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
qui sublati sunt ante tempus suum, et fluvius subvertit fundamentum eorum?
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Qui dicebant Deo: Recede a nobis: et quasi nihil posset facere Omnipotens, æstimabant eum,
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
cum ille implesset domos eorum bonis: quorum sententia procul sit a me.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Videbunt justi, et lætabuntur, et innocens subsannabit eos:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
nonne succisa est erectio eorum? et reliquias eorum devoravit ignis?
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Acquiesce igitur ei, et habeto pacem, et per hæc habebis fructus optimos.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Suscipe ex ore illius legem, et pone sermones ejus in corde tuo.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Si reversus fueris ad Omnipotentem, ædificaberis, et longe facies iniquitatem a tabernaculo tuo.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
Dabit pro terra silicem, et pro silice torrentes aureos.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Eritque Omnipotens contra hostes tuos, et argentum coacervabitur tibi.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Tunc super Omnipotentem deliciis afflues, et elevabis ad Deum faciem tuam.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Rogabis eum, et exaudiet te, et vota tua reddes.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Decernes rem, et veniet tibi, et in viis tuis splendebit lumen.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Qui enim humiliatus fuerit, erit in gloria, et qui inclinaverit oculos, ipse salvabitur.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Salvabitur innocens: salvabitur autem in munditia manuum suarum.]

< Ayuba 22 >