< Ayuba 22 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
데만 사람 엘리바스가 대답하여 가로되
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
사람이 어찌 하나님께 유익하게 하겠느냐? 지혜로운 자도 스스로 유익할 따름이니라
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
네가 의로운들 전능자에게 무슨 기쁨이 있겠으며 네 행위가 온전한들 그에게 무슨 이익이 있겠느냐?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
하나님이 너를 책망하시며 너를 심문하심이 너의 경외함을 인함이냐
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
네 악이 크지 아니하냐 네 죄악이 극하니라
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
까닭 없이 형제의 물건을 볼모 잡으며 헐벗은 자의 의복을 벗기며
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
갈한 자에게 물을 마시우지 아니하며 주린 자에게 식물을 주지 아니하였구나
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
권세 있는 자가 토지를 얻고 존귀한 자가 거기서 사는구나
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
네가 과부를 공수로 돌아가게 하며 고아의 팔을 꺾는구나
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
이러므로 올무들이 너를 둘러있고 두려움이 홀연히 너를 침범하며
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
어두움이 너로 보지 못하게 하고 창수가 너를 덮느니라
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
하나님이 높은 하늘에 계시지 아니하냐? 보라! 별의 높음이 얼마나 높은가
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
그러나 네 말은 하나님이 무엇을 아시며 흑암 중에서 어찌 심판하실 수 있으랴
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
빽빽한 구름이 그를 가리운즉 그가 보지 못하시고 궁창으로 걸어다니실 뿐이라 하는구나
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
네가 악인의 밟던 옛적 길을 지키려느냐?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
그들은 때가 이르기 전에 끊어버리웠고 그 터는 하수로 인하여 함몰되었느니라
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
그들이 하나님께 말하기를 우리를 떠나소서 하며 또 말하기를 전능자가 우리를 위하여 무엇을 하실 수 있으랴 하였으나
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
하나님이 좋은 것으로 그 집에 채우셨느니라 악인의 계획은 나와 판이하니라
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
의인은 보고 기뻐하고 무죄자는 그들을 비웃기를
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
우리의 대적이 끊어졌고 그 남은 것이 불사른 바 되었다 하느니라
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
너는 하나님과 화목하고 평안하라! 그리하면 복이 네게 임하리라!
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
청컨대 너는 그 입에서 교훈을 받고 그 말씀을 네 마음에 두라
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
네가 만일 전능자에게로 돌아가고 또 네 장막에서 불의를 멀리 버리면 다시 흥하리라
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
네 보배를 진토에 버리고 오빌의 금을 강 가의 돌에 버리라
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
그리하면 전능자가 네 보배가 되시며 네게 귀한 은이 되시리니
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
이에 네가 전능자를 기뻐하여 하나님께로 얼굴을 들 것이라
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
너는 그에게 기도하겠고 그는 들으실 것이며 너의 서원한 것을 네가 갚으리라
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
네가 무엇을 경영하면 이루어질 것이요 네 길에 빛이 비취리라
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
네가 낮춤을 받거든 높아지리라고 말하라 하나님은 겸손한 자를 구원하시느니라
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
무죄한 자가 아니라도 건지시리니 네 손이 깨끗함을 인하여 그런 자가 건지심을 입으리라