< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
是においてテマン人エリパズこたへて曰く
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
人 神を益する事をえんや 智人も唯みづから益する而已なるぞかし
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
なんぢ義かるとも全能者に何の歡喜かあらん なんぢ行爲を全たふするとも彼に何の利益かあらん
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
彼汝の畏懼の故によりて汝を責め汝を鞫きたまはんや
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
なんぢの惡大なるにあらずや 汝の罪はきはまり無し
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
即ち汝は故なくその兄弟の物を抑へて質となし 裸なる者の衣服を剥て取り
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
渇く者に水を與へて飮しめず 饑る者に食物を施こさず
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
力ある者土地を得 貴き者その中に住む
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
なんぢは寡婦に手を空しうして去しむ 孤子の腕は折る
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
是をもて網羅なんぢを環り 畏懼にはかに汝を擾す
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
なんぢ黒暗を見ずや 洪水のなんぢを覆ふを見ずや
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
神は天の高に在すならずや 星辰の巓ああ如何に高きぞや
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
是によりて汝は言ふ 神なにをか知しめさん 豈よく黒雲の中より審判するを得たまはんや
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
濃雲かれを蔽へば彼は見たまふ所なし 唯天の蒼穹を歩みたまふ
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
なんぢ古昔の世の道を行なはんとするや 是あしき人の踐たりし者ならずや
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
彼等は時いまだ至らざるに打絶れ その根基は大水に押流されたり
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
彼ら神に言けらく我儕を離れたまへ 全能者われらのために何を爲ことを得んと
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
しかるに彼は却つて佳物を彼らの家に盈したまへり 但し惡人の計畫は我に與する所にあらず
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
義しき者は之を見て喜び 無辜者は彼らを笑ふ
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
曰く我らの仇は誠に滅ぼされ 其盈餘れる物は火にて焚つくさる
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
請ふ汝神と和らぎて平安を得よ 然らば福祿なんぢに來らん
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
請ふかれの口より教晦を受け その言語をなんぢの心に藏めよ
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
なんぢもし全能者に歸向り且なんぢの家より惡を除き去ば汝の身再び興されん
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
なんぢの寳を土の上に置き オフルの黄金を谿河の石の中に置け
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
然れば全能者なんぢの寳となり汝のために白銀となりたまふべし
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
而してなんぢは又全能者を喜び且神にむかひて面をあげん
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
なんぢ彼に祈らば彼なんぢに聽きたまはん 而して汝その誓願をつくのひ果さん
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
なんぢ事を爲んと定めなばその事なんぢに成ん 汝の道には光照ん
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
其卑く降る時は汝いふ昇る哉と 彼は謙遜者を拯ひたまふべし
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
かれは罪なきに非ざる者をも拯ひたまはん 汝の手の潔淨によりて斯る者も拯はるべし

< Ayuba 22 >