< Ayuba 22 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
そこでテマンびとエリパズは答えて言った、
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
「人は神を益することができるであろうか。賢い人も、ただ自身を益するのみである。
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
あなたが正しくても、全能者になんの喜びがあろう。あなたが自分の道を全うしても、彼になんの利益があろう。
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
神はあなたが神を恐れることのゆえに、あなたを責め、あなたをさばかれるであろうか。
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
あなたの悪は大きいではないか。あなたの罪は、はてしがない。
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
あなたはゆえなく兄弟のものを質にとり、裸な者の着物をはぎ取り、
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
疲れた者に水を飲ませず、飢えた者に食物を与えなかった。
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
力ある人は土地を得、名ある人はそのうちに住んだ。
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
あなたは、やもめをむなしく去らせた。みなしごの腕は折られた。
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
それゆえ、わなはあなたをめぐり、恐怖は、にわかにあなたを驚かす。
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
あなたの光は暗くされ、あなたは見ることができない。大水はあなたをおおうであろう。
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
神は天に高くおられるではないか。見よ、いと高き星を。いかに高いことよ。
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
それであなたは言う、『神は何を知っておられるか。彼は黒雲を通して、さばくことができるのか。
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
濃い雲が彼をおおい隠すと、彼は見ることができない。彼は天の大空を歩まれるのだ』と。
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
あなたは悪しき人々が踏んだいにしえの道を守ろうとするのか。
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
彼らは時がこないうちに取り去られ、その基は川のように押し流された。
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
彼らは神に言った、『われわれを離れてください』と、また『全能者はわれわれに何をなしえようか』と。
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
しかし神は彼らの家を良い物で満たされた。ただし悪人の計りごとはわたしのくみする所ではない。
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
正しい者はこれを見て喜び、罪なき者は彼らをあざ笑って言う、
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
『まことにわれわれのあだは滅ぼされ、その残した物は火で焼き滅ぼされた』と。
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
あなたは神と和らいで、平安を得るがよい。そうすれば幸福があなたに来るでしょう。
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
どうか、彼の口から教を受け、その言葉をあなたの心におさめるように。
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
あなたがもし全能者に立ち返って、おのれを低くし、あなたの天幕から不義を除き去り、
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
こがねをちりの中に置き、オフルのこがねを谷川の石の中に置き、
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
全能者があなたのこがねとなり、あなたの貴重なしろがねとなるならば、
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
その時、あなたは全能者を喜び、神に向かって顔をあげることができる。
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
あなたが彼に祈るならば、彼はあなたに聞かれる。そしてあなたは自分の誓いを果す。
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
あなたが事をなそうと定めるならば、あなたはその事を成就し、あなたの道には光が輝く。
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
彼は高ぶる者を低くされるが、へりくだる者を救われるからだ。
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
彼は罪のない者を救われる。あなたはその手の潔いことによって、救われるであろう」。