< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
ויען אליפז התמני ויאמר
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
הלאל יסכן-גבר-- כי-יסכן עלימו משכיל
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
החפץ לשדי כי תצדק ואם-בצע כי-תתם דרכיך
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
המיראתך יכיחך יבוא עמך במשפט
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
הלא רעתך רבה ואין-קץ לעונתיך
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
כי-תחבל אחיך חנם ובגדי ערומים תפשיט
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
לא-מים עיף תשקה ומרעב תמנע-לחם
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
ואיש זרוע לו הארץ ונשוא פנים ישב בה
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
אלמנות שלחת ריקם וזרעות יתמים ידכא
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
על-כן סביבותיך פחים ויבהלך פחד פתאם
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
או-חשך לא-תראה ושפעת-מים תכסך
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
הלא-אלוה גבה שמים וראה ראש כוכבים כי-רמו
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
ואמרת מה-ידע אל הבעד ערפל ישפוט
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
עבים סתר-לו ולא יראה וחוג שמים יתהלך
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
הארח עולם תשמור-- אשר דרכו מתי-און
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
אשר-קמטו ולא-עת נהר יוצק יסודם
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
האמרים לאל סור ממנו ומה-יפעל שדי למו
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
והוא מלא בתיהם טוב ועצת רשעים רחקה מני
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
יראו צדיקים וישמחו ונקי ילעג-למו
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
אם-לא נכחד קימנו ויתרם אכלה אש
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
הסכן-נא עמו ושלם בהם תבואתך טובה
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
קח-נא מפיו תורה ושים אמריו בלבבך
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
אם-תשוב עד-שדי תבנה תרחיק עולה מאהלך
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
ושית-על-עפר בצר ובצור נחלים אופיר
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
והיה שדי בצריך וכסף תועפות לך
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
כי-אז על-שדי תתענג ותשא אל-אלוה פניך
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
תעתיר אליו וישמעך ונדריך תשלם
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
ותגזר-אמר ויקם לך ועל-דרכיך נגה אור
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
כי-השפילו ותאמר גוה ושח עינים יושע
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
ימלט אי-נקי ונמלט בבר כפיך

< Ayuba 22 >