< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Darauf antwortete Eliphas, der Temaniter, und sprach:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Mag auch ein Mann Gott etwas nützen? Es nützt ja der Verständige nur sich selbst.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Hat der Allmächtige Freude, wenn du gerecht bist? Ist's ihm ein Gewinn, wenn du in Unschuld wandelst?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Straft er dich wegen deiner Gottesfurcht, und geht er darum mit dir ins Gericht?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Sind nicht deine Missetaten groß und deine Schulden ohne Ende?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Du hast wohl deine Brüder gepfändet und den Entblößten die Kleider ausgezogen;
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
vielleicht hast du dem Müden kein Wasser zu trinken gegeben oder dem Hungrigen das Brot versagt.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Der Mächtige hat das Land bekommen, und der Angesehene wohnte darin.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Du hast Witwen leer fortgeschickt und die Arme der Waisen zusammenbrechen lassen.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Darum liegst du in Banden und hat Furcht dich plötzlich überfallen.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Oder siehst du die Finsternis nicht und die Wasserflut, die dich bedeckt?
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Ist Gott nicht himmelhoch? Siehe doch die höchsten Sterne, wie hoch sie stehen!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Und du denkst: «Was weiß Gott! Sollte er hinter dem Dunkel richten?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Die Wolken hüllen ihn ein, daß er nicht sehen kann, und er wandelt auf dem Himmelsgewölbe umher!»
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Willst du den alten Weg befolgen, den die Bösewichte gegangen sind,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
die weggerafft wurden von der Flut, deren Fundament der Strom wegriß,
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
die zu Gott sprachen: «Hebe dich weg von uns!» und «was könnte der Allmächtige einem tun?»
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Und er hatte doch ihre Häuser mit Gütern erfüllt! Doch der Gottlosen Rat sei fern von mir!
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Die Gerechten werden es sehen und sich freuen, und der Unschuldige wird ihrer spotten:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
«Fürwahr, unsere Widersacher werden vertilgt, und das Feuer hat ihren Überrest verzehrt.»
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Befreunde dich doch mit Ihm und mache Frieden! Dadurch wird Gutes über dich kommen.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Nimm doch Belehrung an aus seinem Mund und lege seine Worte in dein Herz!
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Wenn du dich zu dem Allmächtigen kehrst, so wirst du aufgerichtet werden, wenn du die Ungerechtigkeit aus deiner Hütte entfernst.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
Wirf das Gold in den Staub und das Ophirgold zu den Steinen der Bäche,
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
so wird der Allmächtige dein Gold und dein glänzendes Silber sein!
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Dann wirst du dich an dem Allmächtigen ergötzen und dein Angesicht zu Gott erheben;
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
du wirst zu ihm flehen, und er wird dich erhören, und du wirst deine Gelübde bezahlen.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Was du vornimmst, das wird dir gelingen, und ein Licht wird auf deinen Wegen leuchten.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Führen sie abwärts, so wirst du sagen: «Es geht empor!» Und wer die Augen niederschlägt, den wird er retten.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Er wird [selbst] den freilassen, der nicht unschuldig ist: durch die Reinheit deiner Hände wird er entrinnen.

< Ayuba 22 >