< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Eliphas von Theman antwortete und sprach:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Kommt etwa Gotte zu gut des Menschen Thun? Nein, nur sich selber nützt der Fromme!
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Hat der Allmächtige einen Vorteil davon, wenn du rechtschaffen bist?, oder einen Gewinn, wenn du unsträflich wandelst?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Straft er dich etwa wegen deiner Gottesfurcht und zieht dich deshalb vor Gericht?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Ist deine Missethat nicht groß, und endlos deine Verschuldungen?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Denn du pfändetest deine Brüder ohne Anlaß und Halbnackten zogst du die Kleider aus.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Nicht tränktest du mit Wasser den Verschmachteten und dem Hungernden versagtest du das Brot.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Dem Manne der Faust, ihm gehörte das Land, und der Hochangesehene wohnte darin.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Witwen schicktest du mit leeren Händen fort, und der Verwaisten Arme wurden zermalmt.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Deshalb sind rings um dich Schlingen, und ängstigt dich jählings der Schrecken!
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Oder siehst du die Finsternis nicht, und die Wasserflut, die dich bedeckt?
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Ist Gott nicht himmelhoch? Schau der Sterne Gipfel an, wie hoch sie ragen!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Und da willst du sprechen: “Was weiß denn Gott? Kann er durch Wolkendunkel hindurch Gericht halten?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Wolken sind seine Hülle, so daß er nicht sieht, und auf des Himmels Kreis lustwandelt er.”
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Willst du der Vorwelt Bahn einhalten, die die Männer des Frevels gewandelt sind?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
sie, die gepackt wurden vor der Zeit, deren Grund zu einem Strome zerfloß?
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Die zu Gotte sprachen: “Bleib uns fern!” und was könne ihnen der Allmächtige thun?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Und doch erfüllte er mit Segen ihre Häuser - der Gottlosen Gesinnung liegt mir fern!
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Es sehen's die Frommen und freuen sich, und der Schuldlose spottet ihrer:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
“Fürwahr, unser Widersacher ist vernichtet, und ihren Überrest hat das Feuer verzehrt!”
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Befreunde dich nicht mit ihm, so wirst du Frieden haben, dadurch kommt Segen über dich.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Nimm doch aus seinem Munde Belehrung an und birg seine Worte in deinem Herzen.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Wenn du dich zum Allmächtigen bekehrst, dich demütigst, wenn du die Sünde aus deinem Zelt entfernst -
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
ja, wirf in den Staub das Brucherz und zu der Bäche Kieseln das Ophirgold! -
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
so wird der Allmächtige dein Erz sein und dir als strahlendes Silber gelten.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Ja, dann wirst du am Allmächtigen deine Wonne haben und dein Antlitz zu Gott erheben.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Flehst du zu ihm, so erhört er dich, und deine Gelübde kannst du bezahlen.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Unternimmst du etwas, so gelingt es dir, und über deinen Wegen strahlet Licht.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Wenn sie abwärts führen, so rufst du: Empor! und dem Demütigen hilft er.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Er errettet den Nicht-Schuldlosen: ja, gerettet wird er durch die Reinheit deiner Hände.

< Ayuba 22 >