< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Éliphaz de Théman prit la parole et dit:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Un homme peut-il être utile à Dieu? Non; le sage n’est utile qu’à lui-même.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Si tu es juste, est-ce à l’avantage du Tout-Puissant? Si tu es intègre dans tes voies, qu’y gagne-t-il?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Est-ce par crainte de toi qu’il te châtie, Qu’il entre en jugement avec toi?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Ta méchanceté n’est-elle pas grande? Tes iniquités ne sont-elles pas infinies?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Tu enlevais sans motif des gages à tes frères, Tu privais de leurs vêtements ceux qui étaient nus;
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Tu ne donnais point d’eau à l’homme altéré, Tu refusais du pain à l’homme affamé.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Le pays était au plus fort, Et le puissant s’y établissait.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Tu renvoyais les veuves à vide; Les bras des orphelins étaient brisés.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
C’est pour cela que tu es entouré de pièges, Et que la terreur t’a saisi tout à coup.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Ne vois-tu donc pas ces ténèbres, Ces eaux débordées qui t’envahissent?
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Dieu n’est-il pas en haut dans les cieux? Regarde le sommet des étoiles, comme il est élevé!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Et tu dis: Qu’est-ce que Dieu sait? Peut-il juger à travers l’obscurité?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Les nuées l’enveloppent, et il ne voit rien; Il ne parcourt que la voûte des cieux.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Eh quoi! Tu voudrais prendre l’ancienne route Qu’ont suivie les hommes d’iniquité?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Ils ont été emportés avant le temps, Ils ont eu la durée d’un torrent qui s’écoule.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Ils disaient à Dieu: Retire-toi de nous; Que peut faire pour nous le Tout-Puissant?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Dieu cependant avait rempli de biens leurs maisons. Loin de moi le conseil des méchants!
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Les justes, témoins de leur chute, se réjouiront, Et l’innocent se moquera d’eux:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
Voilà nos adversaires anéantis! Voilà leurs richesses dévorées par le feu!
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Attache-toi donc à Dieu, et tu auras la paix; Tu jouiras ainsi du bonheur.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Reçois de sa bouche l’instruction, Et mets dans ton cœur ses paroles.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Tu seras rétabli, si tu reviens au Tout-Puissant, Si tu éloignes l’iniquité de ta tente.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
Jette l’or dans la poussière, L’or d’Ophir parmi les cailloux des torrents;
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Et le Tout-Puissant sera ton or, Ton argent, ta richesse.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Alors tu feras du Tout-Puissant tes délices, Tu élèveras vers Dieu ta face;
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Tu le prieras, et il t’exaucera, Et tu accompliras tes vœux.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
A tes résolutions répondra le succès; Sur tes sentiers brillera la lumière.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Vienne l’humiliation, tu prieras pour ton relèvement: Dieu secourt celui dont le regard est abattu.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Il délivrera même le coupable, Qui devra son salut à la pureté de tes mains.

< Ayuba 22 >