< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz replied,
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
“(Can anyone be useful to God?/Certainly no one can be useful to God.) [RHQ] Even people who are wise cannot be helpful to God.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
If you were righteous, (would that benefit Almighty [God]?/that certainly would not benefit Almighty [God].) [RHQ] If you had (lived a perfect life/never done anything that is wrong), would that help him?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
“Is it because you have an awesome respect for God that he punishes you? Is that the reason that he puts you on trial?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
No, it certainly must be [RHQ] because you are extremely wicked. It must be that the evil things that you have done are so many that no one can count them!
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
You must have lent money to others and wrongly forced them to give you things to guarantee that they would pay that money back to you; you must have taken all their clothes and left them with nothing to wear.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
You must not have given water to those who were thirsty, and you must have refused to give food to those who were hungry.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Because you were very powerful, you [must have] taken over all the people’s land, and then, being very respected, you have begun to live on that land.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
[When] widows [came to you for help], you [must have] sent [them] away without giving them anything, and you must have oppressed orphans.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Because of all that, now there are pits around you for you to fall into, and suddenly there are things that terrify you and cause you to tremble.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
[It is as though] it has become very dark, with the result that you cannot see anything, and [it is as though] [MET] a flood covers you.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
“[But consider this, Job]: God lives [RHQ] high up in the heavens. From there he [RHQ] looks down on the highest stars.
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
So why do you say, ‘What does God know [about what we are doing]? [He is hidden from us by] dark clouds, so ([how] can he judge us?/he certainly cannot judge us.) [RHQ]’
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
[Do you think that] while he walks on the dome that covers the sky, there are thick clouds around him, with the result that he cannot see [what we do]?
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Will you continue to conduct your life the old way that evil people have done [for many years]?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
They suddenly died while they were still young; they disappeared [like everything disappears when there is] a flood [MET].
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
They kept saying to God, ‘Do not bother us,’ and they also said [defiantly], ‘Almighty [God] can do nothing [RHQ] to [harm] us!’
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
But it was God who filled their houses with good things, so I cannot at all understand why wicked people think like they do.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
“But when God punishes wicked people, and righteous people see that, they are glad, and they laugh, ridiculing the wicked people.
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
They say, ‘Now our enemies have been destroyed, and all [their possessions] that were left have been burned in a fire.’
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
“So, [Job, ] be reconciled to God and make peace with him; if you do that, good things will happen to you.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Allow him to teach you, and keep thinking about what he has told you.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
If you humble yourself and return to God, if you stop doing all the evil things that you have been doing in your house,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
if you throw away your gold, even the fine gold from the dry stream beds in Ophir [land],
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
and if you allow Almighty [God] to be [as precious to you as] your gold and your silver [have been],
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
you will be happy because of your close relationship with God, and you will be able to approach him [IDM] [confidently].
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
You will pray to him, and he will do what you request him to do; you will do the things that you promised him that you would do.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Everything that you decide to do will be successful; [it] will [be as though] a light [is] shining on the road in front of you.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
God humbles those who are proud, but he saves those who are downcast/discouraged.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
God rescues those who (are innocent/have not done things that are wrong), so he will rescue you if you (start doing things that are right/are not guilty [IDM] of doing things that are wrong).”

< Ayuba 22 >