< Ayuba 22 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then answered Eliphaz the Temanite, and said,
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Can a man be profitable unto God? surely he that is wise is profitable unto himself.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Is it any pleasure to the Almighty, that thou art righteous? or is it gain [to him], that thou makest thy ways perfect?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Is it for thy fear [of him] that he reproveth thee, that he entereth with thee into judgment?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Is not thy wickedness great? neither is there any end to thine iniquities.
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
For thou hast taken pledges of thy brother for nought, and stripped the naked of their clothing.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Thou hast not given water to the weary to drink, and thou hast withholden bread from the hungry.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
But as for the mighty man, he had the earth; and the honourable man, he dwelt in it.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Thou hast sent widows away empty, and the arms of the fatherless have been broken.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Therefore snares are round about thee, and sudden fear troubleth thee,
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Or darkness, that thou canst not see, and abundance of waters cover thee.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Is not God in the height of heaven? and behold the height of the stars, how high they are!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
And thou sayest, What doth God know? can he judge through the thick darkness?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Thick clouds are a covering to him, that he seeth not; and he walketh in the circuit of heaven.
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Wilt thou keep the old way which wicked men have trodden?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Who were snatched away before their time, whose foundation was poured out as a stream:
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Who said unto God, Depart from us; and, What can the Almighty do for us?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Yet he fired their houses with good things: but the counsel of the wicked is far from me.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
The righteous see it, and are glad; and the innocent laugh them to scorn:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
[Saying], Surely they that did rise up against us are cut off, and the remnant of them the fire hath consumed.
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Acquaint now thyself with him, and be at peace: thereby good shall come unto thee.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Receive, I pray thee, the law from his mouth, and lay up his words in thine heart.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
If thou return to the Almighty, thou shalt be built up; if thou put away unrighteousness far from thy tents.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
And lay thou [thy] treasure in the dust, and [the gold of] Ophir among the stones of the brooks;
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
And the Almighty shall be thy treasure, and precious silver unto thee.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
For then shalt thou delight thyself in the Almighty, and shalt lift up thy face unto God.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Thou shalt make thy prayer unto him, and he shall hear thee; and thou shalt pay thy vows.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Thou shalt also decree a thing, and it shall be established unto thee; and light shall shine upon thy ways.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
When they cast [thee] down, thou shalt say, [There is] lifting up; and the humble person he shall save.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
He shall deliver [even] him that is not innocent: yea, he shall be delivered through the cleanness of thine hands.