< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then answered Eliphaz the Temanite, and said:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
Can a man be profitable unto God? Or can he that is wise be profitable unto Him?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Is it any advantage to the Almighty, that thou art righteous? Or is it gain to Him, that thou makest thy ways blameless?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Is it for thy fear of Him that He reproveth thee, that He entereth with thee into judgment?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Is not thy wickedness great? And are not thine iniquities without end?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
For thou hast taken pledges of thy brother for nought, and stripped the naked of their clothing.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Thou hast not given water to the weary to drink, and thou hast withholden bread from the hungry.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
And as a mighty man, who hath the earth, and as a man of rank, who dwelleth in it,
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Thou hast sent widows away empty, and the arms of the fatherless have been broken.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Therefore snares are round about thee, and sudden dread affrighted thee,
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Or darkness, that thou canst not see, and abundance of waters cover thee.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Is not God in the height of heaven? And behold the topmost of the stars, how high they are!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
And thou sayest: 'What doth God know? Can He judge through the dark cloud?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Thick clouds are a covering to Him, that He seeth not; and He walketh in the circuit of heaven.'
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Wilt thou keep the old way which wicked men have trodden?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Who were snatched away before their time, whose foundation was poured out as a stream;
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Who said unto God: 'Depart from us'; and what could the Almighty do unto them?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Yet He filled their houses with good things — but the counsel of the wicked is far from me.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
The righteous saw it, and were glad, and the innocent laugh them to scorn:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
'Surely their substance is cut off, and their abundance the fire hath consumed.'
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Acquaint now thyself with Him, and be at peace; thereby shall thine increase be good.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Receive, I pray thee, instruction from His mouth, and lay up His words in thy heart.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
If thou return to the Almighty, thou shalt be built up — if thou put away unrighteousness far from thy tents,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
And lay thy treasure in the dust, and the gold of Ophir among the stones of the brooks;
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
And the Almighty be thy treasure, and precious silver unto thee;
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Then surely shalt thou have thy delight in the Almighty, and shalt lift up thy face unto God.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Thou shalt make thy prayer unto Him, and He will hear thee, and thou shalt pay thy vows;
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Thou shalt also decree a thing, and it shall be established unto thee, and light shall shine upon thy ways.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
When they cast thee down, thou shalt say: 'There is lifting up'; for the humble person He saveth.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
He delivereth him that is innocent, yea, thou shalt be delivered through the cleanness of thy hands.

< Ayuba 22 >