< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Så tog Temaniten Elifaz til Orde og sagde:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
"Gavner et Menneske Gud? Nej, den kloge gavner sig selv.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Har den Almægtige godt af din Retfærd, Vinding af, at din Vandel er ret?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Revser han dig for din Gudsfrygt? Eller går han i Rette med dig derfor?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Er ikke din Ondskab stor og din Brøde uden Ende?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Thi du pantede Brødre uden Grund, trak Klæderne af de nøgne,
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
gav ikke den trætte Vand at drikke og nægted den sultne Brød.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
Den mægtige - hans var Landet, den hædrede boede der.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Du lod Enker gå tomhændet bort, knuste de faderløses Arme.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Derfor var der Snaret omkring dig, og Rædsel ængsted dig brat.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Dit Lys blev Mørke, du kan ej se, og Strømme af Vand går over dig!
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Er Gud ej i højen Himmel? Se Stjernernes Tinde, hvor højt de står!
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Dog siger du: "Hvad ved Gud, holder han Dom bag sorten Sky?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Skyerne skjuler ham, så han ej ser, på Himlens Runding går han!"
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
Vil du følge Fortidens Sti, som Urettens Mænd betrådte,
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
de, som i Utide reves bort, hvis Grundvold flød bort som en Strøm,
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
som sagde til Gud: "Gå fra os! Hvad kan den Almægtige gøre os?"
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Og han havde dog fyldt deres Huse med godt. Men de gudløses Råd er ham fjernt.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
De retfærdige så det og glædede sig, den uskyldige spottede dem:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
For vist, vore Fjender forgik, og Ild fortæred de sidste af dem.
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Bliv Ven med ham og hold Fred. derved vil der times dig Lykke;
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
tag dog mod Lærdom af ham og læg dig hans Ord på Sinde!
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Vender du ydmygt om til den Almægtige, fjerner du Uretten fra dit Telt,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
kaster du Guldet på Jorden, Ofirguldet blandt Bækkenes Sten,
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
så den Almægtige bliver dit Guld, hans Lov dit Sølv,
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
ja, da skal du fryde dig over den Almægtige og løfte dit Åsyn til Gud.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Beder du til ham, hører han dig, indfri kan du, hvad du har lovet;
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
hvad du sætter dig for, det lykkes, det lysner på dine Veje;
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
thi stolte, hovmodige ydmyger han, men hjælper den, der slår Øjnene ned;
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
han frelser uskyldig Mand; det sker ved hans Hænders Renhed!

< Ayuba 22 >