< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Elifaz Temanac progovori tad i reče:
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
“Zar Bogu koristan može biti čovjek? TÓa tko je mudar, sebi samom koristi.
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Zar je Svesilnom milost što si pravedan i zar mu je dobit što si neporočan?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Ili te zbog tvoje pobožnosti kara i zato se hoće s tobom parničiti?
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Nije l' to zbog zloće tvoje prevelike i zbog bezakonja kojim broja nema?
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
Od braće si brao nizašto zaloge i s golih si ljudi svlačio haljine;
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
ti nisi žednoga vodom napojio, uskraćivao si kruh izgladnjelima;
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
otimao si od siromaha zemlju da bi na njoj svog nastanio ljubimca;
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
puštao si praznih ruku udovice i siročadi si satirao ruku.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Eto zašto tebe mreže sad sapinju, zašto te strahovi muče iznenadni.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Svjetlost ti mrak posta i ništa ne vidiš, vode su duboke tebe potopile.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Zar Bog nije u visini nebeskoj i zar zvijezdama tjeme on ne vidi?
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
Ali ti kažeš: 'Što Bog može znati? Kroz oblak tmasti zar što razabire?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Oblaci pogled njegov zaklanjaju, i rubom kruga on hoda nebeskog.'
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
TÓa kaniš li se drevnog držat' puta kojim su išli ljudi nepravedni?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Prije vremena nestadoše oni, bujica im je temelje raznijela.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Zborahu Bogu: 'Nas se ti ostavi! Što nam Svesilni učiniti može?'
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
A on im je dom punio dobrima makar do njega ne držahu ništa.
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
Videć' im propast, klikću pravednici, neporočni se njima izruguju:
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
'Gle, propadoše protivnici naši, što od njih osta, vatra im proždrije!”
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
S Bogom ti se sprijatelji i pomiri, i vraćena će ti opet biti sreća.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Ded prihvati Zakon iz njegovih usta, u srce svoje riječ njegovu usadi.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
Ako se raskajan vratiš Svesilnome i nepravdu iz svog šatora odstraniš,
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
tad ćeš odbaciti zlato u prašinu i ofirsko blago u šljunak potočni.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
Svesilni će postat' tvoje suho zlato, on će biti tvoje gomile srebrene.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
Da, Svesilni bit će tvoje radovanje, i lice ćeš k Bogu dizati slobodno.
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Molit ćeš mu se, i uslišat će tebe, ispunit ćeš što si mu zavjetovao.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
Što god poduzeo, sve će ti uspjeti, i putove će ti obasjavat' svjetlost.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
Jer, on ponizuje ponos oholima, dok u pomoć smjernim očima pritječe.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
Iz nevolje on izbavlja nevinoga; i tebe će spasit' tvoje čiste ruke.”

< Ayuba 22 >