< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job svarade och sade:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hörer dock till min ord, och låter säga eder;
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Hafver tålamod med mig, att jag ock må tala; och görer sedan spott af mig.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Månn jag handla med en mennisko, att min ande icke skulle härutinnan ångse varda?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Vänder eder hit till mig; I skolen förundra eder, och måsten lägga handena på munnen.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
När jag tänker deruppå, så förskräckes jag; och ett bäfvande kommer uppå mitt kött.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Hvi lefva då de ogudaktige, varda gamle, och växa till i ägodelar?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Deras säd är säker omkring dem, och deras afföda är när dem.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Deras hus hafver frid för räddhåga, och Guds ris är icke öfver dem.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Deras oxa släpper man till, ock missgår icke; deras ko kalfvar, och är icke ofruktsam.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Deras unga barn gå ut såsom en hjord, och deras barn springa.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
De fröjda sig med trummor och harpor, och äro glade med pipande;
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
De varda gamle med göda dagar, och förskräckas som nogast ett ögnablick för helvetet; (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
De dock säga till Gud: Gack bort ifrån oss; vi vilje intet veta af dina vägar;
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Ho är den Allsmägtige, att vi honom tjena skole? Eller hvad kan det båta oss, om vi löpe emot honom?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Men si, deras ägodelar stå icke uti deras händer; derföre skall de ogudaktigas sinne vara långt ifrå mig.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Huru varder de ogudaktigas lykta utsläckt; och deras förderf kommer öfver dem? Han skall utskifta jämmer i sine vrede.
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
De skola varda såsom strå för vädret, och såsom agnar, hvilka stormen bortförer.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Gud förvarar hans barnom bedröfvelse; när han skall löna honom, då skall man förnimmat,
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Hans ögon skola se hans förderf, och af dens Allsmägtigas vrede skall han dricka.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Ty ho skall hafva behag till hans hus efter honom? Och hans månaders tal skall näppliga halft blifva.
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Ho vill lära Gud, den ock dömer de höga?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Denne dör frisk och helbregda, rik och säll.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Hans mjölkekar äro full med mjölk, och hans ben varda full med märg.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Men en annan dör med bedröfvada själ, och hafver aldrig ätit i glädje.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Och de ligga tillhopa med hvarannan i jordene, och matkar öfvertäcka dem.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Si, jag känner väl edra tankar, och edor vrånga anslag emot mig.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Ty I sägen: Hvar är Förstans hus? Och hvar äro hyddorna, der de ogudaktige bodde?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Talen I dock derom såsom meniga folket; och veten icke hvad de andras väsende betyder?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Ty den onde varder behållen intill förderfvelsens dag, och intill vredenes dag blifver han.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Ho vill säga hvad han förtjenar, när man det utvärtes anser? Ho vill vedergälla honom hvad han gör?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Men han varder bortdragen till grafvena, och man vaktar efter honom i högomen.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Bäckaslem behagar honom väl, och alla menniskor varda dragna efter honom; och uppå dem, som för honom varit hafva, är intet tal.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Huru trösten I mig så fåfängt, och edor svar finnas dock orätt?

< Ayuba 21 >