< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Entonces Job respondió y dijo:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Presta atención con cuidado a mis palabras; y deja que este sea tu consuelo.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Déjame decir lo que tengo en mente, y después de eso, siguan burlándose de mí.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
En cuanto a mí, ¿mi queja es contra el hombre? entonces para que preguntarse si mi espíritu está angustiado?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Toma nota de mí y llénate de maravilla, ponte la mano en la boca.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Al pensarlo, mi carne tiembla de miedo.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
¿Por qué se da la vida a los malvados? ¿Por qué se vuelven viejos y fuertes en el poder?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Su simiente están establecidos delante de ellos, y su descendencia delante de sus ojos.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Sus casas están libres de temor, y la vara de Dios no viene sobre ellos.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Su buey engendra sin fallar; Su vaca da a luz, sin abortar.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Envían a sus pequeños como un rebaño, y sus hijos disfrutan bailando.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Hacen canciones a los instrumentos de música, y se alegran del sonido de las flautas.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Sus días terminan sin problemas, y de repente bajan al sepulcro. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Aunque dijeron a Dios: Aléjate de nosotros, porque no deseamos el conocimiento de tus caminos.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
¿Quién es él Todopoderoso, para que podamos adorarlo? ¿Y de qué nos sirve hacer oración a él?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
En verdad, ¿no está su bienestar en su poder? El consejo de los malhechores está lejos de mí.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
¿Con qué frecuencia se apaga la luz de los malhechores, o les vienen problemas? ¿Con qué frecuencia su ira les causa dolor?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
¿Con qué frecuencia son dispersados como paja ante el viento, o como la hierba arrebatada por el viento de tormenta?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Tú dices: Dios mantiene el castigo acumulado para sus hijos. ¡Que pague, para que sepa.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
¡Que sus ojos vean su ruina, y que beba de la ira del Todopoderoso!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
¿Qué interés tiene él en su casa después de que muere, cuando se termina el número de sus meses?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
¿Alguien puede enseñar sabiduría a Dios? siendo él, el juez de los que están en lo alto.
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Uno llega a su fin en completo bienestar, lleno de paz y tranquilidad:
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Sus cubetas están llenos de leche, y no hay pérdida de fuerza en sus huesos.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Y otro llega a su fin con un alma amargada, sin haber probado el buen sabor.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Juntos bajan al polvo, y son cubiertos por el gusano.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Mira, soy consciente de tus pensamientos y de tus propósitos violentos contra mí;
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Porque dices: ¿Dónde está la casa del príncipe, y dónde está la tienda del que hace el mal?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
¿No has hecho la pregunta a los viajeros y no tomas nota de su experiencia?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
¿Cómo el hombre malo sale libre en el día de angustia, y tiene la salvación en el día de ira?
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
¿Quién se dirigirá a su cara? y si ha hecho algo, ¿quién lo castiga?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Lo llevan a su último lugar de descanso y lo vigila.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
La tierra del valle que cubre sus huesos es dulce para él, y todos los hombres vienen después de él, y antes de él han ido innumerables.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
¿Por qué, entonces, me das consuelo con palabras en las que no hay ganancia, cuando ves que no hay nada en tus respuestas sino engaño?

< Ayuba 21 >