< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Y respondió Job, y dijo:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Oíd atentamente mi palabra, y sea esto por vuestros consuelos.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Soportadme, y yo hablaré; y después que hubiere hablado, escarneced.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
¿Por ventura hablo yo a algún hombre? Y si es así ¿por qué no se ha de angustiar mi espíritu?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Miradme, y espantaos, y poned la mano sobre la boca.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Aun yo mismo, cuando me acuerdo, me asombro, y toma temblor mi carne.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
¿Por qué viven los impíos, y se envejecen, y aún crecen en riquezas?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Su simiente con ellos, compuesta delante de ellos; y sus renuevos delante de sus ojos.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Sus casas seguras de temor, ni hay azote de Dios sobre ellos.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Sus vacas conciben, no abortan; paren sus vacas, y no malogran su cría.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Salen sus chiquitos como manada de ovejas, y sus hijos andan saltando.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Al son de tamboril y cítara saltan, y se regocijan al son del órgano.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Gastan sus días en bien, y en un momento descienden a la sepultura. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Dicen pues a Dios: Apártate de nosotros, que no queremos el conocimiento de tus caminos.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
¿Quién es el Todopoderoso, para que le sirvamos? ¿Y de qué nos aprovechará que oremos a él?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
He aquí que su bien no está en manos de ellos; el consejo de los impíos lejos esté de mí.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
¡Oh cuántas veces el candil de los impíos es apagado, y viene sobre ellos su contrición, y con su ira Dios les reparte dolores!
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Serán como la paja delante del viento, y como el tamo que arrebata el torbellino.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Dios guardará para los hijos de ellos su violencia; y le dará su pago, para que conozca.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Verán sus ojos su quebranto, y beberá de la ira del Todopoderoso.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Porque ¿qué deleite tendrá el de su casa después de sí, siendo cortado el número de sus meses?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
¿Por ventura enseñará él a Dios sabiduría, juzgando él las alturas?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Este morirá en la fortaleza de su hermosura, todo quieto y pacífico.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Sus senos están llenas de leche, y sus huesos serán regados de tuétano.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Y este otro morirá en amargura de ánimo, y no habiendo comido jamás con gusto.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Igualmente yacerán ellos en el polvo, y gusanos los cubrirán.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
He aquí, yo conozco vuestros pensamientos, y las imaginaciones que contra mí forjáis.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Porque decís: ¿Qué es de la casa del príncipe, y qué de la tienda de las moradas de los impíos?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
¿No habéis preguntado a los que pasan por los caminos, por cuyas señas no negaréis?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Que el malo es guardado del día de la contrición, del día de las iras son llevados.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
¿Quién le denunciará en su cara su camino? Y de lo que él hizo, ¿quién le dará el pago?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Porque él ya será llevado a los sepulcros, y en el montón permanecerá.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Los terrones del arroyo le serán ya dulces; y tras de él será llevado todo hombre, y antes de él han ido innumerables.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
¿Cómo, pues, me consoláis en vano, dado que vuestras respuestas quedan por mentira?

< Ayuba 21 >