< Ayuba 21 >
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
«Å høyr då, høyr på mine ord! Gjev i minsto det til trøyst!
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Lat meg få lov å tala ut, so kann du spotta etterpå.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Klagar eg vel på menneskje? Og hev eg ikkje grunn til harm?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Vend dykk til meg, og ottast so; legg handi so på dykkar munn.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Eg støkk, når eg det kjem i hug; ei bivring gjenom kroppen gjeng.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Kvifor fær dei gudlause liva, auka i magt som åri gjeng?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Dei ser si ætt stå fast ikring deim, dei hev sitt avkjøme for augo.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
I fred stend husi deira trygge, Guds svipa råkar ikkje deim;
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
med heppa parast deira fe, og kyrne kastar aldri kalv.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Dei slepper borni ut som lamb, og gutarne i leiken hoppar;
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Dei syng til trumma og til cither og frygdar seg ved fløyteljod.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
I lukka liver dei si tid og fer so brått til helheim ned. (Sheol )
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Til Gud dei segjer: «Haldt deg burte!» Me vil’kje kjenna dine vegar!
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Kvi skal me tena den Allsterke? Kva gagnar det å be til honom?»
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
«Dei hev’kje lukka si i handi» - Langt burt frå meg med gudlaus råd!
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Når sloknar lampa for gudlause? Når kjem ulukka yver deim? Gjev han deim straff i vreidesmod?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Fer dei vel burt som strå for vind, lik agner som i stormen fyk?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
«Gud gøymer straffi til hans born.» Nei, sjølv skal mannen straffi kjenna!
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Lat han få sjå sitt eige fall og drikka harm frå den Allsterke!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Kva bryr han seg vel um sitt hus, når månadstalet hans er fullt?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Vil nokon hjelpa Gud til kunnskap, han som er domar for dei høgste?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Den eine døyr på velmagts høgd, fullkomleg trygg og fredeleg;
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
hans fat er fulle utav mjølk, og i hans bein er mergen frisk;
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
den andre døyr so beisk i hug, hev ingenting av lukka smaka.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Dei båe vert i moldi lagde, og deira klednad makkar er.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Sjå kor eg kjennar dykkar tankar, og dykkar meinkrokar mot meg.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
De spør: «Kvar er vel stormannshuset? Kvar er det tjeld der gudlause bur?»
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Hev de’kje høyrt av ferdafolk - de trur vel det som dei fortel -:
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
«Den vonde frå ulukka slepp; han berga vert på vreidedagen.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Kven lastar honom for hans ferd? Og straffar honom for hans gjerd?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Han vert til gravi båren burt, og ved hans gravhaug held dei vakt.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Søtt søv han under torv i dal, og i hans far all verdi fer, som tallause gjekk fyre honom.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Det trøystar meg med tome ord; av dykkar svar er sviket att.»