< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Da tok Job til orde og sa:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hør aktsomt på mitt ord og la dette være den trøst I yder mig!
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Tål mig, så jeg kan få tale, og når jeg har talt, kan du spotte.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Mon min klage gjelder et menneske? Eller hvorfor skulde min ånd ikke bli utålmodig?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Vend eder til mig og bli forferdet og legg hånd på munn!
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Kommer jeg det i hu, så forferdes jeg, og mitt kjød gripes av skjelving.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Hvorfor blir de ugudelige i live, blir gamle og tiltar endog i velmakt?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
De ser sine barn trives omkring sig, og sine efterkommere har de for sine øine.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Deres hus er sikre mot redsler, og Guds ris kommer ikke over dem.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Hans okse parrer sig og spiller ikke, hans ku kalver og kaster ikke i utide.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
De slipper sine barn ut som småfeet, og deres smågutter hopper omkring.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
De synger til tromme og citar, og de gleder sig ved fløitens lyd.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
De lever sine dager i lykke, og i et øieblikk farer de ned til dødsriket. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Og dog sa de til Gud: Vik fra oss! Vi har ikke lyst til å kjenne dine veier.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Hvad er den Allmektige, at vi skulde tjene ham, og hvad gagn skulde vi ha av å vende oss til ham med bønn?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Ja, men deres lykke står ikke i deres egen hånd. - De ugudeliges tanker er langt fra mine tanker.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Hvor ofte utslukkes vel de ugudeliges lampe, og hvor ofte hender det at ulykke kommer over dem? Hvor ofte tildeler han dem vel smerter i sin vrede?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Hvor ofte blir de vel som strå for vinden, som agner stormen fører bort?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Men Gud gjemmer hans straff til hans barn. - Ja, men han burde straffe ham selv, så han fikk kjenne det.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Med egne øine burde han få se sin undergang, og av den Allmektiges vrede burde han få drikke selv.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For hvad bryr han sig om sitt hus efter sin død, når hans måneders tall er ute?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Vil nogen lære Gud visdom, han som dømmer de høieste?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Den ene dør midt i sin velmakt, helt trygg og rolig;
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
hans kar var fulle av melk, og margen i hans ben var saftfull.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Den andre dør med sorg i hjertet og har aldri nytt nogen lykke.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Begge ligger de i støvet, og makk dekker dem.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Se, jeg kjenner eders tanker og de onde råd hvormed I gjør urett mot mig;
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
for I sier: Hvor er tyrannens hus, og hvor er det telt de ugudelige bor i?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Har I aldri spurt dem som har faret vidt omkring? Og I vil vel ikke forkaste deres vidnesbyrd,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
at den onde spares på ulykkens dag, på vredens dag føres han unda.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Hvem foreholder ham hans ferd like i hans ansikt? og når han gjør noget, hvem gjengjelder ham det?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Til graven bæres han med ære, og over gravhaugen holder de vakt.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Søt er hans hvile i dalens muld, og alle mennesker vandrer i hans spor, og det er ikke tall på dem som har gått foran ham.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Hvor kan I da trøste mig med så tom en trøst? Av eders svar blir det bare troløshet tilbake.

< Ayuba 21 >