< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Wasephendula uJobe wathi:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Zwanini lilalele ilizwi lami, lalokho kube zinduduzo zenu.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Ngibekezelelani, ukuthi mina ngikhulume; lemva kokukhuluma kwami lingakloloda.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Mina-ke ukusola kwami kusemuntwini yini? Kodwa uba kunjalo, kungani umoya wami ungekhathazeke?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Ngikhangelani, likhakhamale, libeke isandla phezu komlomo.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Yebo, lapho ngikhumbula, ngitshaywa luvalo, lokuthuthumela kubamba inyama yami.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Ababi baphilelani, babe badala, yebo, bakhule emandleni?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Inzalo yabo izinze phambi kwabo kanye labo, lembewu yabo emehlweni abo.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Izindlu zabo zilokuthula kungelakwesaba, loswazi lukaNkulunkulu kaluphezu kwabo.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Inkunzi yakhe iyakhwela ingaphuthi; inkomokazi yakhe iyazala, ingaphunzi.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Bakhupha abantwanyana babo njengomhlambi, labantwana babo bayagida.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Baphakamisa ilizwi ngesigujana lechacho, bathokoze ngelizwi lomhlanga.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Bachitha insuku zabo ngokuhle, behlele engcwabeni ngokucwayiza kwelihlo. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Babesebesithi kuNkulunkulu: Suka kithi; ngoba kasifisi ulwazi lwendlela zakho.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Uyini uSomandla ukuthi simkhonze? Sizazuzani uba simncenga?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Khangela, okuhle kwabo kakukho esandleni sabo; icebo lababi likhatshana lami.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Kukangaki isibane sababi sicitshwa, kusiza ukuchitheka kwabo phezu kwabo! UNkulunkulu ubabela ubuhlungu elakeni lwakhe.
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Banjengamahlanga phambi komoya, lanjengomule isiphepho esiwuphephulayo.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
UNkulunkulu ubekela abantwana bakhe usizi lwakhe. Uyamvuza, njalo uzakwazi.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Amehlo akhe azabona ukuchitheka kwakhe, anathe okolaka lukaSomandla.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Ngoba iyini intokozo yakhe endlini yakhe emva kwakhe, lapho inani lenyanga zakhe liqunywa?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Kukhona ongafundisa uNkulunkulu ulwazi yini? Ngoba yena wehlulela abaphezulu.
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Lo uyafa esemandleni akhe apheleleyo, yena wonke onwabile, elokuthula.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Iziphathelo zakhe zigcwele uchago, lomnkantsho wamathambo akhe umanzi.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Lomunye ufa elomphefumulo obabayo, engadlanga kokuhle.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Balala ndawonye ethulini, lempethu zibasibekele.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Khangelani, ngiyayazi imicabango yenu, lamacebo eliwaceba limelene lami.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Ngoba lithi: Ingaphi indlu yesiphathamandla? Njalo lingaphi ithente lendawo zababi zokuhlala?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Kalibabuzanga yini abadlula ngendlela, njalo kalinanzeleli iziboniso zabo?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Ukuthi omubi uyekelwa osukwini lokubhujiswa; bazalethwa osukwini lwezintukuthelo.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Ngubani ozamtshela indlela yakhe ebusweni? Ngubani ozamphindisela ngakwenzileyo?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Kanti yena uzasiwa engcwabeni, lilindwe idundulu.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Amagade esihotsha amnandi kuye, njalo udonsa wonke umuntu emva kwakhe, njengoba bengelakubalwa abaphambi kwakhe.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Pho lizangiduduza njani ngeze, ngoba empendulweni zenu kusele inkohliso?

< Ayuba 21 >