< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Allora Giobbe rispose e disse:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
“Porgete bene ascolto alle mie parole, e sia questa la consolazione che mi date.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Sopportatemi, lasciate ch’io parli, e quando avrò parlato tu mi potrai deridere.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Mi lagno io forse d’un uomo? E come farei a non perder la pazienza?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Guardatemi, stupite, e mettetevi la mano sulla bocca.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Quando ci penso, ne sono smarrito, e la mia carne e presa da raccapriccio.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Perché mai vivono gli empi? Perché arrivano alla vecchiaia ed anche crescon di forze?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
La loro progenie prospera, sotto ai loro sguardi, intorno ad essi, e i lor rampolli fioriscon sotto gli occhi loro.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
La loro casa è in pace, al sicuro da spaventi, e la verga di Dio non li colpisce.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Il loro toro monta e non falla, la loro vacca figlia senz’abortire.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Mandan fuori come un gregge i loro piccini, e i loro figliuoli saltano e ballano.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Cantano a suon di timpano e di cetra, e si rallegrano al suon della zampogna.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Passano felici i loro giorni, poi scendono in un attimo nel soggiorno dei morti. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Eppure, diceano a Dio: “Ritirati da noi! Noi non ci curiamo di conoscer le tue vie!
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Che è l’Onnipotente perché lo serviamo? che guadagneremo a pregarlo?”
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Ecco, non hanno essi in mano la loro felicita? (lungi da me il consiglio degli empi!)
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Quando avvien mai che la lucerna degli empi si spenga, che piombi loro addosso la ruina, e che Dio, nella sua ira, li retribuisca di pene?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Quando son essi mai come paglia al vento, come pula portata via dall’uragano?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
“Iddio”, mi dite, “serba castigo pei figli dell’empio”. Ma punisca lui stesso! che lo senta lui,
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
che vegga con gli occhi propri la sua ruina, e beva egli stesso l’ira dell’Onnipotente!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
E che importa all’empio della sua famiglia dopo di lui, quando il numero dei suoi mesi e ormai compiuto?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
S’insegnerà forse a Dio la scienza? a lui che giudica quelli di lassù?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
L’uno muore in mezzo al suo benessere, quand’è pienamente tranquillo e felice,
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
ha i secchi pieni di latte, e fresco il midollo dell’ossa.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
L’altro muore con l’amarezza nell’anima, senz’aver mai gustato il bene.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Ambedue giacciono ugualmente nella polvere, e i vermi li ricoprono.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Ah! li conosco i vostri pensieri, e i piani che formate per abbattermi!
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Voi dite: “E dov’è la casa del prepotente? dov’è la tenda che albergava gli empi?”
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Non avete dunque interrogato quelli che hanno viaggiato? Voi non vorrete negare quello che attestano;
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
che, cioè, il malvagio è risparmiato nel dì della ruina, che nel giorno dell’ira egli sfugge.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Chi gli rimprovera in faccia la sua condotta? Chi gli rende quel che ha fatto?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Egli è portato alla sepoltura con onore, e veglia egli stesso sulla sua tomba.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Lievi sono a lui le zolle della valle; dopo, tutta la gente segue le sue orme; e, anche prima, una folla immensa fu come lui.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Perché dunque m’offrite consolazioni vane? Delle vostre risposte altro non resta che falsità”.

< Ayuba 21 >