< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Et Job prit la parole, et dit:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Écoutez attentivement mes discours, et que cela me tienne lieu de vos consolations!
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Supportez-moi, et je parlerai; et, après que j'aurai parlé, tu te moqueras.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Mais est-ce à un homme que s'adresse ma plainte? Et comment ne perdrais-je pas toute patience?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Regardez-moi, et soyez étonnés, et mettez la main sur la bouche.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Quand j'y pense, je suis éperdu, et un frisson saisit ma chair.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Pourquoi les méchants vivent-ils, vieillissent-ils, et croissent-ils en force?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Leur postérité s'établit devant eux, avec eux, et leurs rejetons sont sous leurs yeux.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Leurs maisons sont en paix, à l'abri de la crainte, et la verge de Dieu n'est pas sur eux.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Leur taureau n'est jamais impuissant, leur génisse vêle et n'avorte pas.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Ils font courir devant eux leurs enfants comme un troupeau, et leur progéniture bondit.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Ils chantent avec le tambourin et la harpe, ils s'égaient au son du hautbois,
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Ils passent leurs jours dans le bonheur, et ils descendent au Sépulcre en un moment. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Et cependant ils ont dit à Dieu: “Éloigne-toi de nous, nous ne voulons pas connaître tes voies.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Qu'est-ce que le Tout-Puissant, pour que nous le servions? Et que gagnerions-nous à le prier? “
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Voici, leur bonheur n'est-il pas en leurs mains? (Que le conseil des méchants soit loin de moi! )
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Combien de fois arrive-t-il que la lampe des méchants s'éteigne, que leur ruine vienne sur eux, que Dieu leur partage leurs lots dans sa colère,
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Qu'ils soient comme la paille au souffle du vent, et comme la balle enlevée par le tourbillon?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Vous dites: “Dieu réserve la peine à ses enfants; “mais qu'Il le punisse lui-même, afin qu'il le sente!
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Qu'il voie de ses propres yeux sa ruine, qu'il boive la colère du Tout-Puissant!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Car, que lui importe sa maison après lui, quand le nombre de ses mois est tranché?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Enseignerait-on la science à Dieu, lui qui juge ceux qui sont élevés?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
L'un meurt au sein du bien-être, tout à son aise et en repos.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Ses flancs sont chargés de graisse, et ses os comme abreuvés de mœlle;
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Un autre meurt dans l'amertume de son âme, n'ayant jamais goûté le bonheur:
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Ils sont couchés ensemble dans la poussière, et les vers les couvrent.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Voici, je connais vos pensées et les desseins que vous formez contre moi.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Car vous dites: Où est la maison de l'homme opulent, et où est la tente, demeure des méchants?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
N'avez-vous jamais interrogé les voyageurs, et n'avez-vous pas reconnu, par leurs témoignages,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Qu'au jour de la calamité, le méchant est épargné, et qu'au jour des colères, il est éloigné?
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Qui lui représente en face sa conduite, et qui lui rend ce qu'il a fait?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Il est porté au tombeau, et, sur le tertre, il veille encore.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Les mottes de la vallée lui sont légères; après lui, suivent à la file tous les hommes, et devant lui, la foule est innombrable.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Comment donc me donnez-vous des consolations vaines? De vos réponses, ce qui reste, c'est la perfidie.

< Ayuba 21 >