< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Alors Job prit la parole et dit:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Ecoutez, écoutez mes paroles, que j’aie, du moins, cette consolation de vous.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Permettez-moi de parler à mon tour, et, quand j’aurai parlé, vous pourrez vous moquer.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Est-ce contre un homme que se porte ma plainte? Comment donc la patience ne m’échapperait elle pas?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Regardez-moi et soyez dans la stupeur, et mettez la main sur votre bouche.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Quand j’y pense, je frémis; et un frissonnement saisit ma chair.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Pourquoi les méchants vivent-ils, et vieillissent-ils, accroissant leur force?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Leur postérité s’affermit autour d’eux, leurs rejetons fleurissent à leurs yeux.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Leur maison est en paix, à l’abri de la crainte; la verge de Dieu ne les touche pas.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Leur taureau est toujours fécond, leur génisse enfante et n’avorte pas.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Ils laissent courir leurs enfants comme un troupeau, leurs nouveau-nés bondissent autour d’eux.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Ils chantent au son du tambourin et de la cithare, ils se divertissent au son du chalumeau.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Ils passent leurs jours dans le bonheur, et ils descendent en un instant au schéol. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Pourtant ils disaient à Dieu: « Retire-toi de nous; nous ne désirons pas connaître tes voies.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Qu’est-ce que le Tout-Puissant, pour que nous le servions? Que gagnerions-nous à le prier? »
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Leur prospérité n’est-elle pas dans leur main? — Toutefois, loin de moi le conseil de l’impie! —
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Voit-on souvent s’éteindre la lampe des impies, la ruine fondre sur eux, et Dieu leur assigner un lot dans sa colère?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Les voit-on comme la paille emportée par le vent, comme la glume enlevée par le tourbillon?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
« Dieu, dites-vous, réserve à ses enfants son châtiment!... » Mais que Dieu le punisse lui-même pour qu’il le sente,
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
qu’il voie de ses yeux sa ruine, qu’il boive lui-même la colère du Tout-Puissant!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Que lui importe, en effet, sa maison après lui, une fois que le nombre de ses mois est tranché?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Est-ce à Dieu qu’on apprendra la sagesse, à lui qui juge les êtres les plus élevés?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
L’un meurt au sein de sa prospérité, parfaitement heureux et tranquille,
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
les flancs chargés de graisse, et la mœlle des os remplie de sève.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
L’autre meurt, l’amertume dans l’âme, sans avoir goûté le bonheur.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Tous deux se couchent également dans la poussière, et les vers les couvrent tous deux.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Ah! Je sais bien quelles sont vos pensées, quels jugements iniques vous portez sur moi.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Vous dites: « Où est la maison de l’oppresseur! Qu’est devenue la tente qu’habitaient les impies? »
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
N’avez-vous donc jamais interrogé les voyageurs, et ignorez-vous leurs remarques?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Au jour du malheur, le méchant est épargné; au jour de la colère, il échappe au châtiment.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Qui blâme devant lui sa conduite? Qui lui demande compte de ce qu’il a fait?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
On le porte honorablement au tombeau; et on veille sur son mausolée.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
les glèbes de la vallée lui sont légères, et tous les hommes y vont à sa suite, comme des générations sans nombre l’y ont précédé.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Que signifient donc vos vaines consolations? De vos réponses il ne reste que perfidie.

< Ayuba 21 >