< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
And Job answereth and saith: —
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hear ye diligently my word, And this is your consolation.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Bear with me, and I speak, And after my speaking — ye may deride.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
I — to man [is] my complaint? and if [so], wherefore May not my temper become short?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Turn unto me, and be astonished, And put hand to mouth.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Yea, if I have remembered, then I have been troubled. And my flesh hath taken fright.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Wherefore do the wicked live? They have become old, Yea, they have been mighty in wealth.
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Their seed is established, Before their face with them, And their offspring before their eyes.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their houses [are] peace without fear, Nor [is] a rod of God upon them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
His bullock hath eaten corn, and doth not loath. His cow bringeth forth safely, And doth not miscarry.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
They send forth as a flock their sucklings, And their children skip,
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
They lift [themselves] up at timbrel and harp, And rejoice at the sound of an organ.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
They wear out in good their days, And in a moment [to] Sheol go down. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
And they say to God, 'Turn aside from us, And the knowledge of Thy ways We have not desired.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
What [is] the Mighty One that we serve Him? And what do we profit when we meet with Him?'
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Lo, not in their hand [is] their good, (The counsel of the wicked Hath been far from me.)
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
How oft is the lamp of the wicked extinguished, And come on them doth their calamity? Pangs He apportioneth in His anger.
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
They are as straw before wind, And as chaff a hurricane hath stolen away,
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
God layeth up for his sons his sorrow, He giveth recompense unto him — and he knoweth.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
His own eyes see his destruction, And of the wrath of the Mighty he drinketh.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For what [is] his delight in his house after him, And the number of his months cut off?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
To God doth [one] teach knowledge, And He the high doth judge?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
This [one] dieth in his perfect strength, Wholly at ease and quiet.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
His breasts have been full of milk, And marrow his bones doth moisten.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
And this [one] dieth with a bitter soul, And have not eaten with gladness.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Together — on the dust they lie down, And the worm doth cover them over.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Lo, I have known your thoughts, And the devices against me ye do wrongfully.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
For ye say, 'Where [is] the house of the noble? And where the tent — The tabernacles of the wicked?'
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Have ye not asked those passing by the way? And their signs do ye not know?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
That to a day of calamity is the wicked spared. To a day of wrath they are brought.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Who doth declare to his face his way? And [for] that which he hath done, Who doth give recompence to him?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
And he — to the graves he is brought. And over the heap a watch is kept.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Sweet to him have been the clods of the valley, And after him every man he draweth, And before him there is no numbering.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
And how do ye comfort me [with] vanity, And in your answers hath been left trespass?

< Ayuba 21 >