< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job replied,
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
“Listen to what I say, all [three] of you; that is the only thing that you can do that will comfort me.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Be patient with me, and allow me to speak. Then, after I am finished speaking, you can continue to make fun of me.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
“It is certainly not [RHQ] people against whom I am complaining, [but God] And it is certainly [RHQ] right for me to be impatient!
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Look at me! Does what you see not cause you to be appalled and to put your hands over your mouths [and say no more]?
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
When I think about [what has happened to me], I am frightened and my entire body shakes.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
“[But let me ask this: ] ‘Why do wicked people continue to live, and become prosperous, and not die until they are very old?’
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
They have their children around them, and they watch them while they [grow up and] start to live in their own houses, and they enjoy their grandchildren.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Wicked people live in their own houses without being afraid, and God does not punish [MTY] them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their bulls always mate with the cows successfully, and the cows give birth to calves and never miscarry.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Wicked people send their young children outside [to play], and the children play [happily] like [SIM] lambs [in a pasture].
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Some children dance and sing, while others shake tambourines and play lyres, and they are happy when they hear people playing flutes.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Wicked people enjoy having good things all the time that they are alive, and they die quietly/peacefully and go down to the place of the dead. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
While they are alive, they say to God, ‘Do not bother us; we do not want to know how you want us to conduct our lives!
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Why do you, Almighty God, think that we should serve you? (What advantage do we get if we pray to you?/It is useless for us to pray to you.) [RHQ]’
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Think about it: Wicked people think that it is because of what they have done that they have become prosperous, but I do not understand why they think like that.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
(“How often does it happen that wicked people die [MET] before they are old?/Very seldom do wicked people die [MET] before they are old.) [RHQ] (Do they ever experience disasters?/They seldom experience disasters.) [RHQ] (Does God ever punish them because of being very angry with them?/God never punishes them because of being very angry with them.) [RHQ]
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
[He does not blow] them away like wind blows away straw; they are never carried off by a whirlwind.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
You say, ‘When people have committed sins, God waits and punishes their children because of those sins;’ but [I say that] God should punish those who sin, [not their children, ] in order that the sinners will know [that it is because of their own sins that they are being punished].
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
I hope/wish that wicked people will experience themselves being destroyed, that they will experience being punished by an angry Almighty God.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
After wicked people are dead, they are not at all concerned [RHQ] about what happens to their families [MTY].
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
“Since God judges [everyone, ] even those that are in heaven, (who can teach God anything?/certainly no one can teach God anything.) [RHQ]
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Some people die while they are very healthy, while they are peaceful, when they are not afraid of anything.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Their bodies are fat; their bones are strong.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Other people die being very miserable; they have never experienced good things happening to them.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
But both rich and poor people die and are buried, and maggots eat their bodies. [Everyone dies, so it is clear that dying is not always the punishment for being wicked].
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
“Listen, I know what you [three] are thinking. I know the evil things that you plan to do to me.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
You say, ‘What happened to the tents in which wicked people were living? The houses of evil rulers have been destroyed!’
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
But have you never inquired of people who travel much? Do you not believe their reports about what they have seen,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
that wicked people usually do not suffer at the time when there are great disasters; that wicked people are the ones who are rescued when God is angry [and punishes people] [MTY]?
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
There is no one [RHQ] who accuses wicked people, and there is no one who (pays them back/gives them the punishment that they deserve) for all the evil things that they have done.
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
The corpses of wicked people are carried to their graves, and people are put there to guard those graves.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
A huge number [HYP] of people go to the grave site. Some go in front of the procession and some come behind. And the clods of dirt thrown on the graves of those wicked people who have died are like a nice blanket.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
“So how can you console me by talking nonsense? Every reply that you make is full of lies!”

< Ayuba 21 >