< Ayuba 21 >
But Job answered and said,
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hear diligently my speech, and let this be your consolations.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Suffer me that I may speak; and after that I have spoken, mock on.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
As for me, [is] my complaint to man? and if [it were so], why should not my spirit be troubled?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Mark me, and be astonished, and lay [your] hand upon [your] mouth.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Even when I remember I am afraid, and trembling taketh hold on my flesh.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Wherefore do the wicked live, become old, yea, are mighty in power?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Their seed is established in their sight with them, and their offspring before their eyes.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their houses [are] safe from fear, neither [is] the rod of God upon them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their bull gendereth, and faileth not; their cow calveth, and casteth not her calf.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
They send forth their little ones like a flock, and their children dance.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
They take the timbrel and harp, and rejoice at the sound of the organ.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
They spend their days in wealth, and in a moment go down to the grave. (Sheol )
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Therefore they say unto God, Depart from us; for we desire not the knowledge of thy ways.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
What [is] the Almighty, that we should serve him? and what profit should we have, if we pray unto him?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Lo, their good [is] not in their hand: the counsel of the wicked is far from me.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
How oft is the candle of the wicked put out! and [how oft] cometh their destruction upon them! [God] distributeth sorrows in his anger.
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
They are as stubble before the wind, and as chaff that the storm carrieth away.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
God layeth up his iniquity for his children: he rewardeth him, and he shall know [it].
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
His eyes shall see his destruction, and he shall drink of the wrath of the Almighty.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For what pleasure [hath] he in his house after him, when the number of his months is cut off in the midst?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Shall [any] teach God knowledge? seeing he judgeth those that are high.
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
One dieth in his full strength, being wholly at ease and quiet.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
His breasts are full of milk, and his bones are moistened with marrow.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
And another dieth in the bitterness of his soul, and never eateth with pleasure.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
They shall lie down alike in the dust, and the worms shall cover them.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Behold, I know your thoughts, and the devices [which] ye wrongfully imagine against me.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
For ye say, Where [is] the house of the prince? and where [are] the dwelling places of the wicked?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Have ye not asked them that go by the way? and do ye not know their tokens,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
That the wicked is reserved to the day of destruction? they shall be brought forth to the day of wrath.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Who shall declare his way to his face? and who shall repay him [what] he hath done?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Yet shall he be brought to the grave, and shall remain in the tomb.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
The clods of the valley shall be sweet unto him, and every man shall draw after him, as [there are] innumerable before him.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
How then comfort ye me in vain, seeing in your answers there remaineth falsehood?