< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
But Job answered and said,
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hear ye, hear ye my words, that I may not have this consolation from you.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Raise me, and I will speak; then ye shall not laugh me to scorn.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
What! is my reproof of man? and why should I not be angry?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Look upon me, and wonder, laying your hand upon your cheek.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
For even when I remember, I am alarmed, and pains seize my flesh.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Wherefore do the ungodly live, and grow old even in wealth?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Their seed is according to [their] desire, and their children are in [their] sight.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Their houses are prosperous, neither [have they] any where [cause for] fear, neither is there a scourge from the Lord upon them.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Their cow does not cast her calf, and their [beast] with young is safe, and does not miscarry.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
And they remain as an unfailing flock, and their children play before [them], taking up the psaltery and harp;
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
and they rejoice at the voice of a song.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
And they spend their days in wealth, and fall asleep in the rest of the grave. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Yet [such a man] says to the Lord, Depart from me; I desire not to know thy ways.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
What is the Mighty One, that we should serve him? and what profit is there that we should approach him?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
For their good things were in [their] hands, but he regards not the works of the ungodly.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Nevertheless, the lamp of the ungodly also shall be put out, and destruction shall come upon them, and pangs of vengeance shall seize them.
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
And they shall be as chaff before the wind, or as dust which the storm has taken up.
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Let his substance fail [to supply] his children: [God] shall recompense him, and he shall know it.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Let his eyes see his own destruction, and let him not be saved by the Lord.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
For his desire is in his house with him, and the number of his months has been suddenly cut off.
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Is it not the Lord who teaches understanding and knowledge? and does not he judge murders?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
One shall die in his perfect strength, and wholly at ease and prosperous;
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
and his inwards are full of fat, and his marrow is diffused [throughout him].
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
And another dies in bitterness of soul, not eating any good thing.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
But they lie down in the earth together, and corruption covers them.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
So I know you, that ye presumptuously attack me:
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
so that ye will say, Where is the house of the prince? and where is the covering of the tabernacles of the ungodly?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Ask those that go by the way, and do not disown their tokens.
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
For the wicked hastens to the day of destruction: they shall be led away for the day of his vengeance.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Who will tell him his way to his face, whereas he has done [it]? who shall recompense him?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
And he has been led away to the tombs, and he has watched over the heaps.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
The stones of the valley have been sweet to him, and every man shall depart after him, and [there are] innumerable [ones] before him.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
How then do ye comfort me in vain? whereas I have no rest from your molestation.

< Ayuba 21 >