< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job antwoordde, en sprak:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Luistert aandachtig naar wat ik ga zeggen; En dat uw troost zich daartoe bepale!
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Laat mij uitspreken op mijn beurt, Wanneer ik klaar ben, kunt ge spotten!
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Heb ik me soms over mensen beklaagd, Of heb ik geen grond, om mismoedig te zijn?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Ziet mij aan, en staat verstomd, En legt uw hand op de mond!
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Wanneer ik er aan denk, sta ik verbijsterd, En huivert mijn vlees:
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
"Waarom blijven de bozen in leven Worden zij oud en groeien in kracht?"
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Hun kroost gedijt voor hun aanschijn, Hun geslacht houdt stand voor hun ogen;
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Hun huizen zijn veilig en zonder vrees, Gods roede valt er niet op neer.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Hun stier bespringt en bevrucht, Hun koeien kalven en hebben geen misdracht;
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Als een kudde laten ze hun jongens naar buiten, En hun kinderen springen rond.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Ze zingen bij pauken en citer, Vermaken zich bij de tonen der fluit;
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Ze slijten hun dagen in weelde, En dalen in vrede ten grave. (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Toch zeggen ze tot God: Blijf verre van ons, We willen uw wegen niet kennen!
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Wat is de Almachtige, dat we Hem zouden dienen; Wat baat het ons, te smeken tot Hem?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Ligt hun geluk niet in hun eigen hand, Bemoeit Hij Zich wel met de plannen der bozen?
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Hoe dikwijls gaat de lamp der bozen wel uit, En stort er rampspoed op hen neer? Hoe dikwijls vernielt Hij de slechten in zijn toorn, Grijpen de weeën hen aan in zijn gramschap;
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Worden zij als stro voor de wind, Als kaf, opgejaagd door de storm?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Gij zegt: God wreekt zijn misdaad op zijn kinderen, En zal hem zo zijn wraak laten voelen!
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Maar zijn eigen ogen moesten zijn rampspoed aanschouwen, Zelf moest hij de toorn van den Almachtige drinken!
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Want wat bekommert hij zich om zijn gezin na zijn dood, Wanneer het getal zijner maanden ten einde is?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Zou men soms God de les willen lezen, Hij, die de hemelingen richt?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
En de een gaat dood, geheel voldaan, Volkomen gelukkig en rustig,
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Zijn lenden vol vet, Het merg in zijn beenderen nog fris.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
De ander sterft met een verbitterd gemoed, Zonder ooit het geluk te hebben gesmaakt!
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Tezamen liggen ze neer in het stof, Door de wormen bedekt!
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Zeker, ik ken uw gedachten, En de bedenkingen, die gij tegen mij aanvoert;
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Gij zegt: "Waar is het huis van den tyran, Waar de tent, waar de bozen in wonen?"
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Hebt gij de reizigers dan nooit ondervraagd, Of aanvaardt gij hun getuigenis niet:
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
"De boze blijft gespaard op de dag van verderf, En ontsnapt op de dag van de gramschap!"
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Wie houdt hem zijn wandel voor ogen, Wie zet hem betaald wat hij deed?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Hij wordt ten grave gedragen, En een tombe houdt er de wacht.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Zacht ligt hij neer Op de kluiten in het dal; Heel de wereld trekt achter hem aan, Talloos velen lopen uit voor zijn stoet.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Wat is uw vertroosting dus schraal, Uw antwoord anders dan leugens!

< Ayuba 21 >