< Ayuba 21 >
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Poslouchejte pilně řeči mé, a bude mi to za potěšení od vás.
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Postrpte mne, abych i já mluvil, a když odmluvím, posmívejž se.
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Zdaliž já před člověkem naříkám? A poněvadž jest proč, jakž nemá býti ssoužen duch můj?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Pohleďte na mne, a užasněte se, a položte prst na ústa.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Ano já sám, když rozvažuji své bídy, tedy se děsím, a spopadá tělo mé hrůza.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Proč bezbožní živi jsou, k věku starému přicházejí, též i bohatnou?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Símě jejich stálé jest před oblíčejem jejich s nimi, a rodina jejich před očima jejich.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Domové jejich bezpečni jsou před strachem, aniž metla Boží na nich.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Býk jejich připouštín bývá, ale ne na prázdno; kráva jejich rodí, a nepotracuje plodu.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Vypouštějí jako stádo maličké své, a synové jejich poskakují.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Povyšují hlasu při bubnu a harfě, a veselí se k zvuku muziky.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol )
Tráví v štěstí dny své, a v okamžení do hrobu sstupují. (Sheol )
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
Kteříž říkají Bohu silnému: Odejdi od nás, nebo známosti cest tvých neoblibujeme.
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Kdo jest Všemohoucí, abychom sloužili jemu? A jaký toho zisk, že bychom se modlili jemu?
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
Ale pohleď, že není v moci jejich štěstí jejich, pročež rada bezbožných vzdálena jest ode mne.
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Často-liž svíce bezbožných hasne? Přichází-liž na ně bída jejich? Poděluje-liž je bolestmi Bůh v hněvě svém?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
Bývají-liž jako plevy před větrem, a jako drtiny, kteréž zachvacuje vicher?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
Odkládá-liž Bůh synům bezbožníka nepravost jeho? Odplacuje-liž jemu tak, aby to znáti mohl,
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
A aby viděly oči jeho neštěstí jeho, a prchlivost Všemohoucího že by pil?
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
O dům pak jeho po něm jaká jest péče jeho, když počet měsíců jeho bude umenšen?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Zdali Boha silného kdo učiti bude umění, kterýž sám vysokosti soudí?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Tento umírá v síle dokonalosti své, všelijak bezpečný a pokojný.
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
Prsy jeho plné jsou mléka, a mozk kostí jeho svlažován bývá.
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
Jiný pak umírá v hořkosti ducha, kterýž nikdy nejídal s potěšením.
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
Jednostejně v prachu lehnou, a červy se rozlezou.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Aj, známť myšlení vaše, a chytrosti, kteréž proti mně neprávě vymýšlíte.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Nebo pravíte: Kde jest dům urozeného? A kde stánek příbytků bezbožných?
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Což jste se netázali jdoucích cestou? Zkušení-liž aspoň jejich nepovolíte,
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Že v den neštěstí ochranu mívá bezbožný, v den, pravím, rozhněvání přistřín bývá?
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Kdo jemu oznámí zjevně cestu jeho? Aneb za to, co činil, kdo jemu odplatí?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
A však i on k hrobu vyprovozen bude, a tam zůstane.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Sladnou jemu hrudy údolí, nadto za sebou všecky lidi táhne, těch pak, kteříž ho předešli, není počtu.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Hle, jak vy mne marně troštujete, nebo v odpovědech vašich ne zůstává než faleš.