< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Entonces Zofar el Naamatita respondió y dijo:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
Por esta causa, mis pensamientos me inquietan y me impulsan.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Tengo que escuchar los reproches de mi desgracia, y él espíritu de mi entendimiento me hace responder.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
¿Sabes esto de los primeros tiempos, cuando el hombre fue puesto en la tierra,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
¿Que el orgullo del pecador es corto, y el gozo del malvado, pero por un minuto?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Aunque él es elevado a los cielos, y su cabeza sube a las nubes;
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Al igual que él estiércol, llega a su fin para siempre: los que lo han visto dicen: ¿Dónde está?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Él se fue como un sueño, y no se le vuelve a ver; va en vuelo como una visión de la noche.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
El ojo que lo vio no lo ve más; y su lugar ya no tiene conocimiento de él.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Sus hijos favorecen a los pobres y sus manos le devuelvan su riqueza.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Sus huesos están llenos de fuerza joven, pero caerá a la tumba.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Aunque el mal es dulce en su boca, y él lo guarda en secreto bajo su lengua;
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
Aunque lo cuida, y no lo deja ir, sino que lo mantiene quieto en su boca;
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
Su comida se amarga en su estómago; El veneno de las serpientes está dentro de él.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Él toma la riqueza como alimento, y la vomita; Es expulsada de su estómago por Dios.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Toma el veneno de las serpientes en su boca, la lengua de la serpiente es la causa de su muerte.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Ni vera los ríos, las corrientes de miel y leche.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Se ve obligado a devolver el fruto de su trabajo, restituirá de acuerdo a lo que tomo; no tiene alegría en el beneficio de su comercio.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Porque ha sido cruel con los pobres, apartándose de ellos en sus problemas; porque tomó una casa por la fuerza que no levantó;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
No hay paz para él en su riqueza, ni salvación para él en aquellas cosas en que se deleitó.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Nunca tuvo suficiente para su deseo; Por esta causa, su bienestar llegará rápidamente a su fin.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Aun cuando su riqueza es grande, está lleno de bastimento, será angustiado, la mano de todos los malvados se vuelve contra él.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Cuando esté comiendo, Dios descargará su ira sobre él, haciéndolo caer sobre él como la lluvia.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Puede ir en vuelo desde la lanza de hierro, pero la flecha de la proa de bronce lo atravesará;
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Lo está sacando, y sale de su espalda; y su punto brillante sale de su costado; es vencido por él terror.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Toda su riqueza está almacenada para la oscuridad; un fuego no hecho por el hombre envía destrucción sobre él, y sobre él que queda en su casa.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Los cielos descubren su pecado, y la tierra da testimonio contra él.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
El producto de su riqueza se perderá en el día que Dios desborde su ira.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Esta es la recompensa del hombre malo, y la herencia que Dios le ha dado.

< Ayuba 20 >