< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Y respondió Sofar Naamatita, y dijo:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
Por cierto mis pensamientos me hacen responder, y por tanto me apresuro.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
El castigo de mi vergüenza he oído, y el espíritu de mi inteligencia me hace responder.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
¿Esto no sabes que fue siempre, desde el tiempo que fue puesto el hombre sobre la tierra:
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
Que la alegría de los impíos es breve, y el gozo del hipócrita, por un momento?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Si subiere hasta el cielo su altura, y su cabeza tocare en las nubes,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Como su mismo estiércol perecerá para siempre: los que le vieren, dirán: ¿Qué es de él?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Como sueño volará, y no será hallado; e irse ha como una visión nocturna.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
El ojo que le viere, nunca más le verá: ni su lugar le verá más.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Sus hijos pobres andarán rogando, y sus manos tornarán lo que él robó.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Sus huesos están llenos de sus mocedades: y con él serán sepultadas en el polvo.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Si el mal se endulzó en su boca, si lo ocultaba debajo de su lengua:
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
Si le parecía bien, y no lo dejaba; mas antes lo detenía entre su paladar:
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
Su comida se mudará en sus entrañas: hiel de áspides [se tornará] dentro de él.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Comió haciendas, mas vomitarlas ha: de su vientre las sacará Dios.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Veneno de áspides chupará: lengua de víbora le matará.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
No verá los arroyos, las riberas de los ríos de miel y de manteca.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Restituirá el trabajo ajeno conforme a la hacienda que tomó: y no tragará, ni gozará.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Por cuanto molió, dejó pobres: robó casas, y no las edificó;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Por tanto él no sentirá sosiego en su vientre, ni escapará con su codicia.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
No quedó nada que no comiese: por tanto su bien no será durable.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Cuando fuere lleno su bastimento, tendrá angustia, toda mano del trabajado le acometerá.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Cuando se pusiere a henchir su vientre, Dios enviará sobre él la ira de su furor; y lloverá sobre él y sobre su comida.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Huirá de las armas de hierro, y pasarle ha el arco de acero.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Desvainará, y sacará saeta de su aljaba, y saldrá resplandeciendo por su hiel: sobre él vendrán terrores.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Todas tinieblas están guardadas para sus secretos, fuego no soplado le devorará: su sucesor será quebrantado en su tienda.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Los cielos descubrirán su iniquidad: y la tierra estará contra él.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Los renuevos de su casa serán trasportados; y serán derramados en el día de su furor.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Esta es la parte que Dios apareja al hombre impío; y esta es la heredad que Dios le señala por su palabra.

< Ayuba 20 >