< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Potem je odgovoril Cofár Naámčan in rekel:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
»Zato mi moje misli povzročajo, da odgovorim in zaradi tega hitim.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Slišal sem preverjanje svoje graje in duh mojega razumevanja mi povzroča, da odgovorim.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Mar ne veš tega od davnine, odkar je bil človek postavljen na zemljo,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
da je zmagoslavje zlobnega kratko, radost hinavca pa le za trenutek?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Čeprav se njegova odličnost vzpenja do neba in njegova glava sega do oblakov,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
se bo vendarle pogubil za vedno, kot njegov lastni iztrebek. Tisti, ki so ga videli, bodo rekli: ›Kje je?‹
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Odletel bo proč kakor sanje in ne bo ga najti. Da, pregnan bo kakor nočno videnje.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
Tudi oko, ki ga je videlo, ga ne bo več videlo niti ga njegov kraj ne bo več gledal.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Njegovi otroci bodo iskali, da ugodijo revnemu in njegove roke bodo obnovile njihove dobrine.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Njegove kosti so polne greha iz njegove mladosti, ki se bodo ulegle z njim v prah.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Čeprav je zlobnost sladka v njegovih ustih, čeprav to skriva pod svojim jezikom,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
čeprav temu prizanaša in tega ne zapusti, temveč to mirno drži znotraj svojih ust,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
je vendar njegova hrana v njegovi notranjosti spremenjena, to je žolč kober znotraj njega.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Pogoltnil je bogastva in ponovno jih bo izbljuval. Bog jih bo izvrgel iz njegovega trebuha.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Sesal bo strup kober, gadov jezik ga bo ubil.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Ne bo videl rek, poplav, potokov iz meda in masla.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
To, za kar se je trudil, bo povrnil in tega ne bo pogoltnil. Glede na njegovo imetje bo povračilo in v tem se ne bo veselil.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Ker je zatiral in zapustil ubogega, ker je nasilno odvzel hišo, ki je ni zgradil,
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
zagotovo ne bo čutil spokojnosti v svojem trebuhu, ne bo rešil od tega, kar si je želel.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Ničesar ne bo ostalo od njegove hrane, zato noben človek ne bo gledal za njegovimi dobrinami.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
V polnosti svoje zadostnosti bo v stiskah; vsaka roka zlobnega bo prišla nadenj.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Ko si namerava napolniti svoj trebuh, bo Bog nadenj vrgel razjarjenost svojega besa in ta bo deževala nadenj, medtem ko jé.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Pobegnil bo pred železnim orožjem in lok iz jekla ga bo prebodel.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Ta je izvlečen in prihaja iz telesa. Da, lesketajoč meč prihaja iz njegovega žolča; strahote so nad njim.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Vsa tema bo skrita v njegovih skritih krajih. Ogenj, ki se ni razgorel, ga bo požrl; slabo bo šlo s tistim, ki je ostal v njegovem šotoru.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Nebesa bodo razodela njegovo krivičnost in zemlja se bo dvignila zoper njega.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Donos njegove hiše bo odšel in njegove dobrine bodo odtekle na dan njegovega besa.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
To je delež zlobnemu človeku od Boga in od Boga določena mu dediščina.«

< Ayuba 20 >