< Ayuba 20 >
1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
И отвечал Софар Наамитянин и сказал:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
размышления мои побуждают меня отвечать, и я поспешаю выразить их.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Упрек, позорный для меня, выслушал я, и дух разумения моего ответит за меня.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Разве не знаешь ты, что от века, - с того времени, как поставлен человек на земле, -
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
веселье беззаконных кратковременно, и радость лицемера мгновенна?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Хотя бы возросло до небес величие его, и голова его касалась облаков, -
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
как помет его, на веки пропадает он; видевшие его скажут: где он?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Как сон, улетит, и не найдут его; и, как ночное видение, исчезнет.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
Глаз, видевший его, больше не увидит его, и уже не усмотрит его место его.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Сыновья его будут заискивать у нищих, и руки его возвратят похищенное им.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Кости его наполнены грехами юности его, и с ним лягут они в прах.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Если сладко во рту его зло, и он таит его под языком своим,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
бережет и не бросает его, а держит его в устах своих,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
то эта пища его в утробе его превратится в желчь аспидов внутри его.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Имение, которое он глотал, изблюет: Бог исторгнет его из чрева его.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Змеиный яд он сосет; умертвит его язык ехидны.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Не видать ему ручьев, рек, текущих медом и молоком!
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Нажитое трудом возвратит, не проглотит; по мере имения его будет и расплата его, а он не порадуется.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Ибо он угнетал, отсылал бедных; захватывал дома, которых не строил;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
не знал сытости во чреве своем и в жадности своей не щадил ничего.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Ничего не спаслось от обжорства его, зато не устоит счастье его.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
В полноте изобилия будет тесно ему; всякая рука обиженного поднимется на него.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Когда будет чем наполнить утробу его, Он пошлет на него ярость гнева Своего и одождит на него болезни в плоти его.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Убежит ли он от оружия железного, - пронзит его лук медный;
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
станет вынимать стрелу, - и она выйдет из тела, выйдет, сверкая сквозь желчь его; ужасы смерти найдут на него!
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Все мрачное сокрыто внутри его; будет пожирать его огонь, никем не раздуваемый; зло постигнет и оставшееся в шатре его.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Небо откроет беззаконие его, и земля восстанет против него.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Исчезнет стяжание дома его; все расплывется в день гнева Его.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Вот удел человеку беззаконному от Бога и наследие, определенное ему Вседержителем!