< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Então Zophar, o Naamathite, respondeu,
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
“Portanto, meus pensamentos me respondem, mesmo por causa da minha pressa que está em mim.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Ouvi a repreensão que me envergonha. O espírito da minha compreensão me responde.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Don você não sabe isto dos velhos tempos, desde que o homem foi colocado na terra,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
que o triunfo dos ímpios é curto, a alegria dos ímpios, mas por um momento?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Embora sua altura se eleve até os céus, e sua cabeça alcança as nuvens,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
yet ele perecerá para sempre como seu próprio esterco. Aqueles que o viram dirão: “Onde ele está?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Ele vai voar como um sonho, e não será encontrado. Sim, ele será afugentado como uma visão da noite.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
O olho que o viu não o verá mais, nem seu lugar o verá mais.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Seus filhos buscarão o favor dos pobres. Suas mãos devolverão sua riqueza.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Seus ossos estão cheios de sua juventude, mas a juventude se deitará com ele no pó.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
“Embora a maldade seja doce em sua boca, embora ele o esconda debaixo da língua,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
though ele o poupa, e não o deixa ir, mas mantenha-o ainda dentro de sua boca,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
yet sua comida em seu intestino está virada. É o veneno da cobra dentro dele.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Ele engoliu riquezas, e as vomitará novamente. Deus vai expulsá-los de sua barriga.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
He irá sugar o veneno da cobra. A língua da víbora vai matá-lo.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Ele não vai olhar para os rios, os fluxos de mel e manteiga.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Ele vai restaurar aquilo pelo qual trabalhou e não vai engolir. Ele não se regozijará de acordo com a substância que recebeu.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Pois ele tem oprimido e abandonado os pobres. Ele tirou violentamente uma casa e não vai construí-la.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
“Porque ele não conhecia nenhum sossego dentro dele, ele não salvará nada daquilo em que ele se deleita.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Não havia mais nada que ele não devorasse, portanto, sua prosperidade não perdurará.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Na plenitude de sua suficiência, a angústia o ultrapassará. A mão de todos que estão na miséria virá sobre ele.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Quando ele estiver prestes a encher sua barriga, Deus lançará sobre ele a ferocidade de sua ira. Vai chover sobre ele enquanto ele come.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
He irá fugir da arma de ferro. A seta de bronze o atingirá através dele.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Ele o tira para fora, e ele sai de seu corpo. Sim, o ponto cintilante sai de seu fígado. Os terrores estão sobre ele.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Toda a escuridão é depositada para seus tesouros. Um incêndio não planejado o devorará. Ele consumirá o que for deixado em sua tenda.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Os céus revelarão sua iniqüidade. A terra se levantará contra ele.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
O aumento de sua casa irá partir. Eles se apressarão no dia de sua ira.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Esta é a porção de um homem perverso de Deus, a herança a ele designada por Deus”.

< Ayuba 20 >