< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Então respondeu Sofar, o naamathita, e disse:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
Por isso é que os meus pensamentos me fazem responder, e portanto me apresso.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Eu ouvi a reprehensão, que me envergonha, mas o espirito do meu entendimento responderá por mim.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Porventura não sabes isto, que foi desde todo o tempo, desde que o homem foi posto sobre a terra?
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
A saber: que o jubilo dos impios é breve, e a alegria dos hypocritas como d'um momento?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Ainda que a sua altura subisse até ao céu, e a sua cabeça chegasse até ás nuvens,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Comtudo como o seu proprio esterco perecerá para sempre: e os que o viam dirão: Onde está?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Como um sonho vôa, e não será achado, e será afugentado como uma visão da noite.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
O olho que já o viu jamais o verá, nem olhará mais para elle o seu logar.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Os seus filhos procurarão agradar aos pobres, e as suas mãos restaurarão a sua fazenda.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Os seus ossos se encherão dos seus peccados occultos, e juntamente se deitarão com elle no pó.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Ainda que o mal lhe seja doce na bocca, e elle o esconda debaixo da sua lingua,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
E o guarde, e o não deixe, antes o retenha no seu paladar,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
Comtudo a sua comida se mudará nas suas entranhas; fel d'aspides será interiormente.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Enguliu fazendas, porém vomitalas-ha; do seu ventre Deus as lançará.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Veneno d'aspides sorverá; lingua de vibora o matará.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Não verá as correntes, os rios e os ribeiros de mel e manteiga.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Restituirá do seu trabalho, e não o engulirá: conforme ao poder de sua mudança, e não saltará de gozo.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Porquanto opprimiu, desamparou os pobres, e roubou a casa que não edificou.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Porquanto não sentiu socego no seu ventre; da sua tão desejada fazenda coisa nenhuma reterá.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Nada lhe sobejará do que coma; pelo que a sua fazenda não será duravel.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Estando já cheia a sua abastança, estará angustiado: toda a mão dos miseraveis virá sobre elle
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Haja porém ainda de que possa encher o seu ventre; comtudo Deus mandará sobre elle o ardor da sua ira, e a fará chover sobre elle quando elle fôr a comer.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Ainda que fuja das armas de ferro, o arco d'aço o atravessará.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Desembainhada a espada, sairá do seu corpo, e resplandecendo virá do seu fel: e haverá sobre elle assombros.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Toda a escuridão se occultará nos seus esconderijos: um fogo não assoprado o consumirá: e com o que ficar na sua tenda irá mal.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Os céus manifestarão a sua iniquidade: e a terra se levantará contra elle.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
As rendas de sua casa serão transportadas: no dia da sua ira todas se derramarão.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Esta, da parte de Deus, é a porção do homem impio: e, da parte de Deus, a herança dos seus ditos.

< Ayuba 20 >