< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Da tok Sofar fra Na'ama til orde og sa:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
Derfor legger mine tanker mig svaret i munnen, og derfor stormer det i mig;
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
hånende tilrettevisning må jeg høre, og min ånd gir mig svar ut fra min innsikt.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Vet du da ikke at slik har det vært fra evighet, fra den tid mennesker blev satt på jorden,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
at de ugudeliges jubel er kort, og den gudløses glede bare varer et øieblikk?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Stiger enn hans stolthet til himmelen, og når enn hans hode til skyen,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
så går han dog likesom sitt skarn til grunne for evig; de som så ham, spør: Hvor er han?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Som en drøm flyr han bort, og ingen finner ham mere; han jages bort som et nattesyn.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
Det øie som så ham, ser ham ikke mere, og hans sted skuer ham ikke lenger.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Hans barn må søke småfolks yndest, og hans hender må gi hans gods tilbake.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Hans ben var fulle av ungdomskraft, men nu ligger den med ham i støvet.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Smaker enn det onde søtt i hans munn, skjuler han det under sin tunge,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
sparer han på det og slipper det ikke, men holder det tilbake under sin gane,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
så blir dog hans mat omskapt i hans innvoller og blir til ormegift i hans liv.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Han slukte gods, og han må spy det ut igjen; Gud driver det ut av hans buk.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Ormegift må han innsuge; huggormens tunge dreper ham.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Han skal ikke få se bekker, elver av honning og elver av melk.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Han må gi tilbake det han har tjent, og får ikke nyte det; meget gods har han vunnet, men han får liten glede av det.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
For han knuste småfolk og lot dem ligge der; han rante hus til sig, men får ikke bygge dem om;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
han kjente aldri ro i sitt indre; han skal ikke slippe unda med sine skatter.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Det var intet som undgikk hans grådighet; derfor varer ikke hans lykke.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Midt i hans rikdom blir det trangt for ham; hver nødlidende vender sin hånd mot ham.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
For å fylle hans buk sender Gud sin brennende vrede mot ham og lar sin mat regne på ham.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Flykter han for våben av jern, så gjennemborer en bue av kobber ham.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Når han så drar pilen ut av sin rygg, og den lynende odd kommer frem av hans galle, da faller dødsredsler over ham.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Alt mørke er opspart for hans vel gjemte skatter; en ild som intet menneske puster til, fortærer ham; den eter det som er igjen i hans telt.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Himmelen åpenbarer hans misgjerning, og jorden reiser sig mot ham.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Det han har samlet i sitt hus, føres bort, det skylles bort på Guds vredes dag.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Dette er den lodd som et ugudelig menneske får av Gud, den arv som er tilkjent ham av den Allmektige.

< Ayuba 20 >