< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Alors, répondant, Sophar, le Naamathite, dit:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
C’est pour cela que mes différentes pensées se succèdent, et que mon esprit est entraîné dans des sentiments divers.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
J’écouterai la doctrine en vertu de laquelle tu m’accuses, et l’esprit de mon intelligence répondra pour moi.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Ce que je sais être dès le principe, depuis que l’homme a été placé sur la terre,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
C’est que la gloire des impies a été courte et la joie de l’hypocrite comme un moment.
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Si son orgueil s’élève jusqu’au ciel, et que sa tête touche les nues,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Il périra à la fin comme un fumier, et ceux qui l’avaient vu diront: Où est-il?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Comme un songe qui s’envole, on ne le verra plus; il passera comme une vision de nuit.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
L’œil qui l’avait vu ne le verra pas; et son lieu ne le regardera plus.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Ses enfants dépériront par l’indigence, et ses mains lui rendront la douleur qu’il a faite aux autres.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Ses os seront remplis des vices de sa jeunesse, et ces vices dormiront avec lui dans la poussière,
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Car, comme le mal est doux à sa bouche, il le cachera sous sa langue.
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
Il le ménagera, et il ne le laissera pas, mais il le tiendra caché dans sa gorge.
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
Son pain dans ses entrailles, au dedans de lui, se changera en fiel d’aspic.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Il vomira les richesses qu’il a dévorées, et Dieu les arrachera de ses entrailles.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Il sucera la tête des aspics, et la langue d’une vipère le tuera.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
(Qu’il ne voie point couler les ruisseaux d’un fleuve, et les torrents de miel et de beurre).
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Il expiera tout ce qu’il a fait, et cependant il ne sera pas consumé; c’est selon les richesses qu’il a acquises qu’il aura à souffrir,
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Parce qu’en les brisant, il a dépouillé les pauvres; il a ravi une maison qu’il n’a pas bâtie.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Son ventre n’a pas été rassasié; et lorsqu’il aura eu ce qu’il avait convoité, il ne pourra pas le posséder.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Il n’est rien resté de ses vivres; et à cause de cela rien ne lui demeurera de ses biens.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Lorsqu’il se sera rassasié, il sera oppressé et étouffé de chaleur, et toute sorte de douleurs fondront sur lui.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Puisse son ventre être rempli, en sorte que Dieu envoie contre lui la colère de sa fureur, et qu’il fasse pleuvoir sur lui ses foudres!
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Il échappera à des armes de fer, mais il sera transpercé par un arc d’airain.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Un glaive tiré et sortant de son fourreau étincellera dans son amertume; d’horribles spectres iront et viendront sur lui.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Toutes sortes de ténèbres sont fermées à ses caches; un feu qui ne s’allume point le dévorera; il sera affligé, se trouvant délaissé dans son tabernacle.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Les cieux révéleront son iniquité, et la terre s’élèvera contre lui.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Les rejetons de sa maison seront exposés à la violence; ils seront enlevés au jour de la fureur de Dieu.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Voilà la part d’un homme impie, faite par Dieu, et l’héritage réservé à ses paroles par le Seigneur.

< Ayuba 20 >