< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Tsophar, de Naama, prit la parole et dit:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
C'est pour cela que mes pensées me poussent à répondre, et c'est pour cette raison que j'ai hâte de le faire:
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
J'ai entendu une leçon outrageante, mais l'esprit tire de mon intelligence une réponse.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Ne sais-tu pas que, de tout temps, depuis que Dieu a mis l'homme sur la terre,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
Le triomphe du méchant est de peu de durée, et la joie de l'impie n'a qu'un moment?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Quand son élévation monterait jusqu'aux cieux, et quand sa tête atteindrait les nues,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Il périra pour toujours, comme son ordure; ceux qui le voyaient diront: Où est-il?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Il s'envolera comme un songe, et on ne le trouvera plus; il s'évanouira comme un rêve de la nuit.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
L'œil qui l'a vu ne le verra plus, et son lieu ne l'apercevra plus.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Ses enfants feront la cour aux pauvres, et ses propres mains restitueront ses biens.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Ses os sont pleins de jeunesse, mais elle reposera avec lui dans la poussière.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Si le mal est doux à sa bouche, s'il le cache sous sa langue,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
S'il le ménage et ne le rejette point, s'il le retient dans son palais,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
Sa nourriture se changera dans ses entrailles, et deviendra dans son sein du fiel d'aspic.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Il a englouti des richesses, et il les vomira; Dieu les arrachera de son ventre.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
Il sucera du venin d'aspic; la langue de la vipère le tuera.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Il ne verra plus les ruisseaux, les fleuves, les torrents de miel et de lait.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
Il rendra le fruit de son travail, et ne l'avalera pas; il restituera à proportion de ce qu'il aura amassé, et ne s'en réjouira pas.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Parce qu'il a foulé, abandonné le pauvre, pillé la maison au lieu de la bâtir;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Parce qu'il n'a pas connu le repos dans son avidité, il ne sauvera rien de ce qu'il a tant désiré;
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Rien n'échappait à sa voracité, c'est pourquoi son bonheur ne durera pas.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Au comble de l'abondance, il sera dans la gêne; les mains de tous les malheureux se jetteront sur lui.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
Il arrivera que pour lui remplir le ventre, Dieu enverra contre lui l'ardeur de sa colère; il la fera pleuvoir sur lui et entrer dans sa chair.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Il fuira devant les armes de fer, l'arc d'airain le transpercera.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
Il arrachera la flèche, et elle sortira de son corps, et le fer étincelant, de son foie; les frayeurs de la mort viendront sur lui.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Toutes les calamités sont réservées à ses trésors, un feu qu'on n'aura pas besoin de souffler le dévorera, et ce qui restera dans sa tente sera consumé.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
Les cieux découvriront son iniquité, et la terre s'élèvera contre lui.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
Le revenu de sa maison sera emporté. Tout s'écoulera au jour de la colère.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
Telle est la part que Dieu réserve à l'homme méchant, tel est l'héritage que Dieu lui assigne.

< Ayuba 20 >