< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar replied,
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
“I am very perturbed about what you have said, so I want to reply very quickly.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
By saying these things you have insulted me, but I know how (OR, because I understand very much) I can reply to you.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
“Do you not know that from long ago, ever since people were first put on the earth,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
wicked people [like you] do not continue to rejoice for a long time, ungodly people are happy only for a (moment/very short time) [HYP]?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
[Even] though their reputation/pride reaches up to the sky and their fame goes up as high as the clouds,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
they will disappear forever, like their own dung, and those who knew them will ask, ‘(Where did they go/What happened to them)?’
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
They will be forgotten like [SIM] a dream is, and they will exist no more. They will vanish, like visions [that people see] during the night.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
Those who saw those people previously will never see them again; even their families [MTY] will not see them any more.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
Their children will be forced to return the valuable things that those children stole from poor people [DOU].
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
Previously their bodies were young and strong, but they will die and [their bodies will] be buried in the ground.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
“Doing wicked things was like having sweet food in their mouths, and they wanted to continue to taste it.
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
And they did not want to stop doing those things,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
[but some day] the evil things that they enjoyed doing will become like food [that they swallow] [and which becomes] as bitter as snake venom.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
Wicked people will not continue to keep the money they have accumulated, like people do not keep the food that they vomit. God takes their wealth from them.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
What wicked people do is [like] [MET] swallowing snake venom; it will kill them like [MET] the bite of a poisonous snake kills people.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
They will not remain alive to see abundant blessings [IDM] [from God], milk and olive oil and honey, that are [so abundant they are] like [MET] a stream that flows by.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
They will be forced to give back the things that they stole from the poor; they will not be able to continue to enjoy those things. They will not remain happy because of what they got from their businesses,
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
because they oppressed poor people and refused to help them, and they took other people’s houses [by cheating them].
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
“They were always greedy and never satisfied. They just keep dreaming about owning more and more things.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
When they finished eating their food, there was never anything left over [because they had greedily eaten it all]; but now their prosperity will end.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
When they are extremely prosperous/wealthy, they will suddenly experience a lot of trouble. (Misery will strike them and crush them [PRS]/They will suffer very greatly).
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
When the wicked people are filling their stomachs, God will show that he is very angry with them and punish them; the punishment [that he gives them] will be like [MET] rain falling on them.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
They will try to escape from [being killed by] iron weapons, but arrows with bronze points will pierce them.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
The arrows will [go completely through their bodies and] stick out of their backs; the shiny points of the arrows will have blood dripping from them, and those wicked people will be terrified.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Their valuable possessions will all be destroyed; a fire that is not lit by humans, [but by God, ] will burn them up and also destroy the things that are left in their tents.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The [angels in] heaven [MTY] will reveal the sins that those wicked people have committed, and [people on] earth will stand up and testify against them.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
When God punishes [MTY] [people], all the possessions in the wicked people’s houses will be carried away by a flood.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
That is what will happen to wicked people [like you]; that is what God has decided will happen to them.”

< Ayuba 20 >