< Ayuba 20 >
1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
And Zophar the Naamathite answers and says:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
“Therefore my thoughts cause me to answer, And because of my sensations in me.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
I hear the discipline of my shame, And the spirit of my understanding causes me to answer:
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Have you known this from antiquity? Since the placing of man on earth?
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
That the singing of the wicked [is] short, And the joy of the profane for a moment,
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Though his excellence goes up to the heavens, He strikes his head against a cloud—
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
He perishes as his own dung forever, His beholders say, Where [is] he?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
He flees as a dream, and they do not find him, And he is driven away as a vision of the night,
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
The eye has not seen him, and does not add. And his place does not behold him again.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
His sons oppress the poor, And his hands give back his wealth.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
His bones have been full of his youth, and it lies down with him on the dust.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Though he sweetens evil in his mouth, hides it under his tongue,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
has pity on it, and does not forsake it, and keeps it back in the midst of his palate,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
his food is turned in his bowels, the bitterness of cobras [is] in his heart.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
He has swallowed wealth, and vomits it. God drives it out from his belly.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
He sucks [the] gall of cobras, the tongue of a viper slays him.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
He does not look on streams, Flowing of brooks of honey and butter.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
He is giving back [what] he labored for, and does not consume [it]; As a bulwark [is] his exchange, and he does not exult.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
For he oppressed—he forsook the poor, He has taken a house away violently, And he does not build it.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
For he has not known ease in his belly. With his desirable thing he does not deliver himself.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
There is not a remnant to his food, Therefore his good does not stay.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
In the fullness of his sufficiency he is constricted. Every perverse hand meets him.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
It comes to pass, at the filling of his belly, He sends forth against him The fierceness of His anger, Indeed, He rains on him in his eating.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
He flees from an iron weapon, A bow of bronze passes through him.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
One has drawn, And it comes out from the body, And a glittering weapon proceeds from his gall. Terrors [are] on him.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
All darkness is hid for his treasures, A fire not blown consumes him, The remnant is broken in his tent.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The heavens reveal his iniquity, And earth is raising itself against him.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
The increase of his house is removed, Poured forth in a day of His anger.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
This [is] the portion of a wicked man from God. And an inheritance appointed him by God.”