< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then answered Zophar the Na'amathite, and said,
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
Even therefore do my inmost thoughts give me an answer, and for this reason do I feel a strong excitement within me.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
Reproof which casteth shame on me must I hear; yet out of my understanding will the spirit give me an answer.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Dost thou know this? from the very beginning of things, from the very time when man was placed upon earth it was,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
That the triumphal shouting of the wicked is ever of but a recent date, and the joy of the hypocrite endureth only for a moment.
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Though his exaltation should mount up to the heavens, and his head should reach unto the clouds;
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Yet when he but turneth round will he vanish for ever; those who have seen him will say, Where is he?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
Like a dream will he fly away, and men will find him no more; yea, he will be chased away like a vision of the night.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
If an eye have surveyed him, it will not do so again, and it will not behold him any more in his place.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
His children will suffer oppression from the indigent, and his hands will have to restore his [ill-gotten] wealth.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
[Now] his bones are full of his youthful vigor; but it will [suddenly] lie down with him in the dust.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
If the evil be sweet in his mouth, he will conceal it under his tongue;
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
He will cherish it, and not forsake it; and hold it back within his palate;
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
His food is thus changed within his bowels, and becometh the venom of asps within him.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
The wealth which he hath swallowed, will he have to vomit up again; God will drive it out of his belly.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
The poison of asps will he have to suck; the viper's tongue will slay him.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
He shall not look with pleasure on streams, on flowing brooks of honey and cream.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
He restoreth what he hath labored for, and will not swallow it down; however much he may have obtained by toil, he will not have any joy of it.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Because he oppressed and forsook the indigent; because he took violently away a house, shall he not rebuild it;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Because he knew not quietness in his bosom, shall he not escape through what is the most precious to him.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Nothing was spared from his craving to eat: therefore shall his wealth not prosper.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
In the fulness of his abundance will distress assail him: every hand of [those he] troubled will come against him.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
In order to fill his belly, [God] will send out against him the fury of his wrath, and will rain it upon him for his eating.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
If he flee from the iron weapon, the brazen bow will strike him through.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
He draweth it, and it cometh out of the body; yea, out of his gall the glittering [arrow] cometh forth: over him come the terrors [of death].
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Entire darkness is laid by for his treasures: a fire not urged by blowing will consume him; it will destroy any one that is left in his tent.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The heavens will lay open his iniquity; and the earth will raise herself up against him.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
The product of his house will be banished, flowing away on the day of his wrath.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
This is the portion of a wicked man from God, and his decreed heritage from God.

< Ayuba 20 >