< Ayuba 20 >
1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar the Naamathite made answer and said,
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
For this cause my thoughts are troubling me and driving me on.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
I have to give ear to arguments which put me to shame, and your answers to me are wind without wisdom.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Have you knowledge of this from early times, when man was placed on the earth,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
That the pride of the sinner is short, and the joy of the evil-doer but for a minute?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Though he is lifted up to the heavens, and his head goes up to the clouds;
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
Like the waste from his body he comes to an end for ever: those who have seen him say, Where is he?
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
He is gone like a dream, and is not seen again; he goes in flight like a vision of the night.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
The eye which saw him sees him no longer; and his place has no more knowledge of him.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
His children are hoping that the poor will be kind to them, and his hands give back his wealth.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
His bones are full of young strength, but it will go down with him into the dust.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Though evil-doing is sweet in his mouth, and he keeps it secretly under his tongue;
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
Though he takes care of it, and does not let it go, but keeps it still in his mouth;
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
His food becomes bitter in his stomach; the poison of snakes is inside him.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
He takes down wealth as food, and sends it up again; it is forced out of his stomach by God.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
He takes the poison of snakes into his mouth, the tongue of the snake is the cause of his death.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
Let him not see the rivers of oil, the streams of honey and milk.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
He is forced to give back the fruit of his work, and may not take it for food; he has no joy in the profit of his trading.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
Because he has been cruel to the poor, turning away from them in their trouble; because he has taken a house by force which he did not put up;
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
There is no peace for him in his wealth, and no salvation for him in those things in which he took delight.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
He had never enough for his desire; for this cause his well-being will quickly come to an end.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
Even when his wealth is great, he is full of care, for the hand of everyone who is in trouble is turned against him.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
God gives him his desire, and sends the heat of his wrath on him, making it come down on him like rain.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
He may go in flight from the iron spear, but the arrow from the bow of brass will go through him;
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
He is pulling it out, and it comes out of his back; and its shining point comes out of his side; he is overcome by fears.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
All his wealth is stored up for the dark: a fire not made by man sends destruction on him, and on everything in his tent.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The heavens make clear his sin, and the earth gives witness against him.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
The produce of his house is taken away into another country, like things given into the hands of others in the day of wrath.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
This is the reward of the evil man, and the heritage given to him by God.