< Ayuba 20 >
1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar the Naamathite replied:
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
“So my anxious thoughts compel me to answer, because of the turmoil within me.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
I have heard a rebuke that insults me, and my understanding prompts a reply.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Do you not know that from antiquity, since man was placed on the earth,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
the triumph of the wicked has been brief and the joy of the godless momentary?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Though his arrogance reaches the heavens, and his head touches the clouds,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
he will perish forever, like his own dung; those who had seen him will ask, ‘Where is he?’
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
He will fly away like a dream, never to be found; he will be chased away like a vision in the night.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
The eye that saw him will see him no more, and his place will no longer behold him.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
His sons will seek the favor of the poor, for his own hands must return his wealth.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
The youthful vigor that fills his bones will lie down with him in the dust.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
Though evil is sweet in his mouth and he conceals it under his tongue,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
though he cannot bear to let it go and keeps it in his mouth,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
yet in his stomach his food sours into the venom of cobras within him.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
He swallows wealth but vomits it out; God will force it from his stomach.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
He will suck the poison of cobras; the fangs of a viper will kill him.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
He will not enjoy the streams, the rivers flowing with honey and cream.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
He must return the fruit of his labor without consuming it; he cannot enjoy the profits of his trading.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
For he has oppressed and forsaken the poor; he has seized houses he did not build.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
Because his appetite is never satisfied, he cannot escape with his treasure.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Nothing is left for him to consume; thus his prosperity will not endure.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
In the midst of his plenty, he will be distressed; the full force of misery will come upon him.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
When he has filled his stomach, God will vent His fury upon him, raining it down on him as he eats.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
Though he flees from an iron weapon, a bronze-tipped arrow will pierce him.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
It is drawn out of his back, the gleaming point from his liver. Terrors come over him.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
Total darkness is reserved for his treasures. A fire unfanned will consume him and devour what is left in his tent.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The heavens will expose his iniquity, and the earth will rise up against him.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
The possessions of his house will be removed, flowing away on the day of God’s wrath.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
This is the wicked man’s portion from God, the inheritance God has appointed him.”