< Ayuba 2 >

1 Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
Så hendte det en dag at Guds sønner kom og stilte sig frem for Herren, og blandt dem kom også Satan og stilte sig frem for Herren.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Og Herren sa til Satan: Hvor kommer du fra? Satan svarte Herren: Jeg har faret og flakket omkring på jorden.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
Da sa Herren til Satan: Har du gitt akt på min tjener Job? For det er ingen på jorden som han - en ulastelig og rettskaffen mann, som frykter Gud og viker fra det onde; ennu er han like ulastelig, og du har uten grunn egget mig til å ødelegge ham.
4 Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
Men Satan svarte Herren: Hud for hud, men alt det en mann har, gir han for sitt liv.
5 Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
Men rekk bare ut din hånd og rør ved hans ben og hans kjøtt! Da vil han visselig si dig farvel like i ditt ansikt.
6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
Da sa Herren til Satan: Se, han er i din hånd; spar bare hans liv!
7 Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
Så gikk Satan bort fra Herrens åsyn, og han slo Job med onde bylder fra fotsålen til issen.
8 Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
Og han tok sig et potteskår og skrapte sig med, der han satt midt i asken.
9 Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
Da sa hans hustru til ham: Holder du dig ennu like ulastelig? Si Gud farvel og dø!
10 Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
Men han svarte: Du taler som en av de uforstandige kvinner; skal vi bare ta imot det gode av Gud og ikke også det onde? Under alt dette syndet Job ikke med sine leber.
11 Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
Da Jobs tre venner fikk høre om all denne ulykke som var kommet over ham, kom de fra hver sitt hjemsted: Elifas fra Teman, Bildad fra Suah og Sofar fra Na'ama; og de avtalte med hverandre å gå til ham for å vise ham medynk og trøste ham.
12 Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
Men da de så op et stykke ifra, kjente de ham ikke, og de brast i gråt og sønderrev sine kapper og kastet støv op imot himmelen, ned over sine hoder.
13 sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.
Og de satt hos ham på jorden i syv dager og syv netter, og ingen talte et ord til ham; for de så at hans pine var såre stor.

< Ayuba 2 >