< Ayuba 2 >
1 Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
Og det skete en Dag, der Guds Børn kom for at fremstille sig for Herren, da kom ogsaa Satan midt iblandt dem for at fremstille sig for Herren.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Da sagde Herren til Satan: Hvorfra kommer du? og Satan svarede Herren og sagde: Fra at gaa omkring i Landet og vandre om derudi.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
Og Herren sagde til Satan: Har du givet Agt paa min Tjener Job? thi der er ingen som han i Landet, en oprigtig og retskaffen Mand, som frygter Gud og viger fra det onde, og han holder endnu fast ved sin Retsindighed; men du har tilskyndet mig imod ham at ødelægge ham uden Aarsag.
4 Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
Da svarede Satan Herren og sagde: Hud for Hud, ja alt det, en Mand har, giver han for sit Liv.
5 Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
Dog udræk nu din Haand og rør ved hans Ben og hans Kød; hvad gælder det, om han ikke skal fornægte dig lige for dit Ansigt?
6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
Og Herren sagde til Satan: Se, han være i din Haand; dog var hans Liv!
7 Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
Da for Satan ud fra Herrens Ansigt og slog Job med onde Bylder fra hans Fodsaal og indtil hans Isse.
8 Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
Og han tog sig et Potteskaar til at skrabe sig med, og han sad midt i Asken.
9 Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
Og hans Hustru sagde til ham: Holder du endnu fast ved din Retsindighed? velsign Gud og dø!
10 Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
Men han sagde til hende: Du taler, ligesom en af de daarlige Kvinder taler; skulde vi alene tage imod det gode af Gud og ikke tage imod det onde? I alt dette syndede Job ikke med sine Læber.
11 Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
Og der Jobs tre Venner hørte al den Ulykke, som var kommen over ham, da kom de, hver fra sit Sted: Themaniten Elifas og Sukiten Bildad og Naamathiten Zofar, og de forenede sig med hverandre for at komme at vise ham Medynk og trøste ham.
12 Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
Men der de opløftede deres Øjne langtfra, da kendte de ham ikke, og de opløftede deres Røst og græd, og de sønderrev hver sin Kappe, og de kastede Støv paa deres Hoveder op imod Himmelen.
13 sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.
Og de sade hos ham paa Jorden syv Dage og syv Nætter, og ingen talte et Ord til ham; thi de saa, at Pinen var saare stor.